Abubuwan da suka faru a Nigeria da sassan duniya kan coronavirus

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma wasu sassan duniya, musamman rahotanni kan annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Watakila mu hana balaguro tsakanin jihohin Nigeria– Lai Mohammed

    Lai Mohammed

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Najeriya ta ce akwai yiwuwar ta hana zirga-zirga tsakanin jihohin kasar a ci gaba da yaki da yaduwar coronavirus a kasar, wadda mutum 51 suka kamu da cutar.

    Ministan Yada Labarai da Al'adu, Lai Mohammed ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja ranar Alhamis, inda ya ce sun dauki tsauraran matakan ne doimin tabbatar cewa gwamnati ba ta gaza ba wurin kare rayukan al'umma.

    "'Yan kasa maza da mata, daga cikin tsauraran matakan da muka dauka akwai hana zirga-zirga tsakanin jihohin kasa, rufe duk tashoshin mota, dakatar da sufurin jirgin kasa, yin amfani da kayayyakin kashe gobara da sauran ababen hawa domin yin feshin magani a birane da kaunyuka," ministan ya fada.

    Ya kara da cewa dama tuni aka dakatar da zirga-zirgar jirgin kasan fasinja a kasa baki daya.

    "Za mu ci gaba da bayar da bayanai kan sabbin matakan da muke dauka, amma ku sani duk matakin da muka dauka na kare muradun kasa ne da 'yan kasa baki daya," in ji Lai Mohammed.

    Har wa yau, ministan ya ce zuwa yanzu akwai wuraren killace jama'a uku a Abuja - mai gado 40 da mai gado 60 da mai gado 160 - sannan kuma suna ci gaba da neman wasu wuraren domin killace wadanda aka samu da cutar a birnin.

    Kazalika, ya ce akwai mutum 4,370 da mahukunta ke bin sawu domin sanin tabbacin ko sun kamu da cutar ko kuma a'a, sannan ya nemi wadanda suka san sun yi mu'amala da masu dauke da ita da su kai kansu ga hukumomi domin yin gwaji.

  2. Coronavirus: Jihar Kaduna ta samar da layin gaggawa

    Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da samar da layin kiran gaggawa da mutane za su iya yi idan an ga wani mai alamun coronavirus.

    Gwamnatin ta sanar da hakan ne a wani sakon Twitter a ranar Alhamis.

    Ta ce a yanzu za a iya samun layin a kullum daga karfe 8.30 na safe zuwa 9 na yamma.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  3. Kasashen G20 za su zuba $5tn a tattalin arzikin duniya

    Kasashe 20 masu karfin tattalin arziki na duniya G20 sun sha alwashin zuba dala tiriliyan biyar a tattalin arzikin duniya a kokarinsu na ceto yanayin da tattalin arzikin ke neman fadawa salkamakon annobar.

    An sanar da hakan ne a karshen wani taron kungiyar G") din da Saudiyya ta karbi bakuncinsa.

  4. Kasashen Turai sun rufe iyakokin juna

    Kasashen Tarayyar Turai sun rufe iyakokinsu bayan shekara 25 da kaddamar da tsarin shiga kasashen juna ba shinge.

    A ranar 26 ga watan Maris din 1995 aka kaddamar da wannan tsari

    Amma a yau bayan 25, sai ga shi kowace kasa ta yankin ta rufe iyakokinta a wani mataki na hana yaduwar annobar coronavirus.

    Hukumar Kula da Iyakoki ta Turai, Frontex, ta wallafa taswirar a shafinta na Twitter da ke nuna matakai daban-daban da aka dauka a nahiyar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  5. Taka tsan-tsan, samun sauki da fatan alheri sun cika zuciyoyin al'ummar Wuhan

    Mr Li

    Asalin hoton, Mr Li

    Mutanen Wuhan na kasar China wadanda a baya yankinsu ne ciibiyar coronavirus, inda cutar ta samo asali, a karshe sun fara koma wa cikin yanayi na nutsuwa bayan da aka shafe wata biyu ba shiga ba fita a birnin.

    Hukumomi a China sun ce za a dage dokar hana tafiye-tafiye a birnin mai mutum miliyan 11 ranar 8 ga watan Afrilu.

    Al'amura sun fara yin sauki - makarantu sun ci gaba da kasancewa a rufe, amma za a dawo da zirga-zirgar ababen hawa a mako mai zuwa, sannan mazauna birnin masu yawan sanya takunkumin rufe fuska tuni suka fara fara fita yawon shakatawa.

    ''Na ji dadi saboda kwana 60 kenan ba mu da 'yancin walwala,'' a cewar Mr Li mai shekara 53 da ke zaune a Wuhan.

    Yana fatan nan gaba kadan zai koma bakin aikinsa a wajen gine-gine. An dakatar da harkar gine-gine don haka ya yi ta rayuwa ne kan dan abin da ya tara a baya, yanzu kuma yana tsananin son gana wa da danginsa da abokansa.

    Amma fa mazauna garin ba sa cikin yanayin da za su yi murna.

    ''Mutane da dama sun mutu, amma har yanzu ana boye gaskiyar zancen. Wuhanda duniya baki daya suna cikin halin radadi,'' in ji Mr Li.

    Wasu suna cikin damuwa kan tsangwamar da mutane ke fuskanta.''Ina jin bakin ciki. Garina ya shiga wani yanayi,'' a cewar wani lauya wanda ba ya so a ambaci sunansa.

    ''Ana nuna wa mutane kyama a cikin kasarsu. Amma me mutanen garin da shi kansa birnin suka yi da suka cancani haka?''

    Akwai kuma fargaba kan yiwuwar sake samun wadanda za su iya kamuwa da cutar da zarar an dage takunkuman.

  6. Ba na dauke da cutar coronavirus – Zainab Shamsuna

    Zainab Shamsuna Ahmed

    Asalin hoton, @ZShamsuna

    Bayanan hoto, Zainab Shamsuna (daga hagu) ta yi kira da a ci gaba da wanke hannu da yin nesa-nesa da juna don kauce wa kamuwa da cutar

    Hankalin Ministar Kudi ta Najeriya Zainab Shamsuna Ahmed ya kwanta bayan gwaji ya nuna ba ta dauke da cutar cornavirus a ranar Alhamis.

    Ministar ta wallafa farin cikinta a shafin Twitter jim kadan bayan ta samu sakamakon.

    "Na ji dadi da sakamaon gwajin Covid-19 da ya nuna ba na dauke da cutar da kuma addu'o'i da damuwar da kuka nuna mani," ministar ta fada.

    A ranar Talata ne dai aka samu rahoton cewa Abba Kyari, shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin Najeriya ya kamu da cutar.

    Rahotanni sun ce shi ma Shugaba Buhari ya yi gwajin amma ba ya dauke da ita.

    "Ina kira ga kowa da kowa da a rika nesa-nesa da juna, a wanke hannaye a-kai-a-kai domin kawo karshen wannan annoba," Zainab Shamsuna ta yi kira.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  7. Sarauniya Elizabeth ta yi ganawar mako-mako da firai minista ta waya

    Sarauniya Elizabeth ta yi ganawar mako-mako da ta saba tsakaninta da Firai Ministan Birtaniya Boris Johnson amma wannan karon ta waya sakamakon coronavirus.

    Sarauniyar ta yi tattaunawar ne daga gidanta na Windsor Castle a ranar Laraba.

    A jiya Laraba ne aka tabbatar dan gidan Sarauniyar wato Yarima Charles ya kamu da cutar.

    Mutum 465 ne suka mutu a Birtaniya sakamakon coronavirus, yayin da 9,500 aka tabbatar sun kamu.

    Kauce wa Instagram
    Ya kamata a bar bayanan Instagram?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da Instagram suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Instagram da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a Instagram

  8. Coronavirus: Yadda ake layin sayen kayan abinci a Afirka ta Kudu

    Afirka ta Kudu

    Asalin hoton, Getty Images

    'Yan kasar Afirk ata Kudu na dandazo a bakin bankuna da shaguna inda suka kafa dogwayen layuka domin sayen kayan masarufu, 'yan awowi kadan kafin fara aiwatar da dokar kulle a kasar.

    Da daren yau Alhamis ne dai dokar za ta fara aiki ga kowa ban da ma'aikata kamar likitoci.

    Wannan alama ce da ke nuna irin zaman zulumi da fargaba da 'yan kasar ke ciki duk kuwa da cewa an ba su tabbacin samun duk abin da suke so.

    Za a rufe gidajen cin abinci da shagunan sayar da barasa. Sai dai shagunan abinci da ma'aikatan tsaro da na lafiya ke amfani da su za su kasance a bude.

  9. Mutum 132 sun kamu da coronavirus a Ghana

    Ghana

    Asalin hoton, Getty Images

    A kasar Ghana na samu sabbin alkaluman mutanen da suka kamu da cutar coronavirus 54.

    Kawo yanzu masu dauke da cutar a fadin kasar sun kai 132.

  10. Nigeria: Wasu na wasa da hankalin hukumomi kan coronavirus

    Hukumar yaki da yaduwar cutuka a Najeriya ta ce ta bibiyi wasu sakonni da kiraye-kiraye kan wani bidiyo a shafin Instagram da wani ya yi cewa yana dauke da cutar coronavirus.

    A cikin bidiyon, mutumin ya yi ikirarin cewa ya yi ta kiran hukumar amma bai same su ba, abin da ya sa ta tuntube shi amma sai ya ce lafiyarsa kalau, wasan barkwanci yake yi.

    Saboda haka ne hukumar ta ce: "Muna kira ga al'umma da su girmama layukan kira da sakonnin gaggawa, kada a yada fargaba."

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  11. Lagos za ta feshe jihar da magani don yakar coronavirus

    Jihar Legas za ta raba kayan feshin magani zuwa lungu da sako na jihar a ci gaba da yaki da annobar coronavirus.

    Mutum shida sun warke daga cikin 32 da ke dauke da coronavirus a Legas, kari a mutum biyu da suka warke tun farko. A Najeriya baki daya mutum 51 ne suka kamu da ita.

    Ya zuwa yanzu dai mutum 43 ne ke fama da cutar a Najeriya.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  12. Dokar hana fita za ta fara aiki a Afirka ta Kudu

    Afirka ta Kudu

    Asalin hoton, Getty Images

    A daren ranar Alhamis ne dokar hana fita za ta soma aiki a kasar Afrika takudu domin dakile bazuwar cutar coranaviirus.

    Kasar ita ce ta fi yawan wadanda suka kamu da cutar a nahiyar Afrika inda yanzu haka mutum sama da 700 ne cutar ta harba.

  13. Coronavirus: Ministar Abuja ta yi gwaji, ta killace kanta

    Ramatu Tijjani

    Asalin hoton, @DrRamatuAliyu

    Karamar Ministar Abuja, babban birnin Tarayyar Najeriya, ta yi gwajin cutar coronavirus.

    Kamar yadda ta wallafa a shafinta na Twitter, Ramatu Tijjani Aliyu ta ce ta yi gwajin ne tare da killace kanta bayan ta hadu da wasu mutane da ke dauke da cutar.

    Zuwa lokacin da ta wallafa wannan sako da karfe 2:50 na ranar Laraba, ministar ta ce lafiyarta kalau ba tare da nuna wata alamar cutar ba.

    Mutum 51 ne ke dauke da coronavirus a Najeriya, mutum daya ya warke, daya ya mutu, a cewar hukumar NCDC mai yaki da yaduwar cutuka.

    Rahotanni daga Jihar Legas na cewa wasu mutum shida sun warke, a cewar wani mataimaki na musamman ga gwamnan Legas.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  14. Coronavirus: Mutum 6 sun warke a Legas

    Mai magana da yawun gwamnan jihar Legas, Tunde Ajayi, ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa an samu mutum shida da suka warke daga cutar coronavirus.

    Hukumar NCDC dai ta sanar da cewa akwai masu coronavirus 32 a jihar Legas.

    Yanzu kenan mutanen da ke dauke da cutar a jihar ta Legas sun kama 26.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  15. Lambar kiran gaggawa a Kano kan coronavirus

    Bayanai kan Coronavirus

    Asalin hoton, NCDC

    Ma'aikatar Lafiya Jihar Kano ta fassara matakan kariya daga annobar coronavirus domin wayar da kan al'umma a jihar.

    Kazalika ma'aiktar lafiyar jihar ta samar da wasu layukan gaggawa da za a kira idan aka samu wani da ke bukatar kulawa.

    Lambobin su ne: 09093995333 09093995444

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  16. Coronavirus: An kashe wani da ke kokarin saka bam a asibiti

    Jama'a

    Asalin hoton, EPA

    'Yan sandan Amurka na FBI sun harbe wani mutum mai shekara 36 yayin da yake yunkurin tashin wani asibiti da bam a Jihar Missouri.

    FBI ta ce Timothy Wilson "hatsabibin mutum ne" wanda ya saba nuna wariyar launin fata da bambancin addini da kiayayya ga gwamnati.

    Ya so ya kai hari wurare da dama, ciki har da wata makaranta cike da dalibai bakaken fata da wurin ibadar Yahudawa da masallaci, a cewar wani rahoton gidan talabijin na NBC.

    Daga karshe dai ya zabi wani asibiti "inda zai jikkata jama'a da yawa" in aka duba "halin da ake ciki na rikicin lafiya," FBI ta bayyana. Ta ce ya tattara dukkanin abin da yake bukata na hada bam din.

    An jikkata Wilson a ranar Talata lokacin da 'yan sanda suka yi kokarin kama shi a Belton, yayin da ya je daukar wata motar da ya yi zaton bam din ne a ciki. "Sai dai babu bam a ciki," in ji FBI.

    NBC ta rawaito cewa wanda ake zargin bai ji dadin yunkurin gwamanati jihar ba na yaki da cutar coronavirus.

  17. Coronavirus: An nemi a yafe wa Afirka bashin da ake bin ta

    Coronavirus

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana ci gaba da kiraye-kiraye ga kasashen da suka ci gaba da su yafe wa kasashen Afirka basukan da suke bin su domin su samu damar yakar annobar coronvirus.

    A farkon makon nan ne dai firai ministan Ethiopia, Abiy Ahmed ya mika wannan bukata ga shugabannin kasashen G20 masu karfin tattalin arziki.

    Kungiyar agaji ta Oxfam ta mika irin wannan bukata ga taron kasashen Tarayyar Turai da ake yi a yau Alhamis ta hanyar intanet.

    Oxfam ta ce kasashen Afirka tuni suke fafutukar yaki da cutar coronavirus da dan abin da suke da shi.

  18. Coronavirus: Wadanda suka mutu a Spain sun kai 4,089

    Bayanai na baya-bayan nan daga kasar Sifaniya na cewa mutum 655 ne suka mutu a cikin awa 24, wanda ya kawo adadin wadanda suka mutu a kasar zuwa 4,089.

    Wadanda aka tabbatar suna dauke da cutar sun kai 56,188.

    Har yanzu birnin Madrid ne cutar ta fi yi wa illa, inda kusan biyu cikin uku na masu cutar ke can. Shi ma yankin Catalonia ya fuskanci karin masu cutar, inda ya bayyana 11,592 da ke dauke da ita.

    A daren jiya Laraba Sifaniya ta kara adadin kwanakin dokar ta-baci har zuwa 12 ga watan Afrilu domin dakile yaduwar cutar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  19. Kenya ta samu mutumin da ya warke daga coronavirus

    Uhuru Kenyatta

    Asalin hoton, Getty Images

    Kenya ta sanar da mutum na farko da ya warke baki daya daga cutar coronavirus.

    Shugaba Uhuru Kenyatta ya kuma bayar da umarnin hana fita, rage albashi da kuma kudin motocin haya a wani mataki na dakile bazuwar cutar a kasar.

    A wani jawabi da ya yi wa 'yan kasar, Kenyatta ya ce bayyana warkewar da mutumin ya yi daga cutar ta coronavirus a matsayin wani labari mai kwarara gwiwa.

    Ya zuwa yanzu dai Kenya na da masu cutar coronavirus 28.

  20. Amurka za ta bai wa kowanne dan kasa dala 1,200 tallafin coronavirus

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    'Yan majalisar Amurka sun amince da dalar Amurka tiriliyan 2 a matsayin tallafin rage radadin cutar coronavirus, wanda ya hada da bai wa dukkan 'yan kasa matasa dala 1,200 kyauta (sama da naira 400,000).

    An samu tsaiko yayin kada kuri'ar amincewa da kudirin dokar sakamakon rikici tsakanin 'yan jam'iyyar Democrats da Republican a kan alfanon da marasa aikin yi za su samu a cikin kudirin.

    Daga cikin abin da kudirin ya kunsa akwai bai wa kusan kowanne baligi dala 1,200 a matsayin tallafi sannan kuma a taimaka wa masu matsakaitan kasuwanci biyan albashin ma'aikatansu.

    Wadanda suka mutu a Amurka sakamakon cutar sun kai 1,000 sannan kuma akwai kusan 70,000 da aka tabbatatar suna dauke da cutar.

    A duniya baki daya, fiye da mutum 21,000 ne suka mutu tun daga sanda annobar ta barke a yankin Hubei na China a watan Disamba. Wadanda suka kamu kuwa sun kusa rabin miliyan.

    Kudancin Nahiyar Turai ne cibiyar annobar a yanzu, inda kasashen Sifaniya da Italiya ke samun daruruwan mamata a kullum.