Abubuwan da suka faru a Nigeria da sassan duniya kan coronavirus

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma wasu sassan duniya, musamman rahotanni kan annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Coronavirus: 'Duk wanda ya ziyarci New York to ya killace kansa'

    Andrew Cuomo

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Amurka ta ce duk wani wanda ya san ya fita daga birnin New York a cikin 'yan kwanakin da suka gabata to ya kebe kansa na mako biyu.

    Birnin shi ne yankin da wannan annoba tafi yaduwa a Amurka da kashi 2 cikin 3 na sabbin alkaluman masu dauke da cutar da aka tabbatar a kasar.

    Akwai fargabar mutanen da ke ziyartar sauran yankunan kasar su sake yada anobar.

    A wani taron manema labarai a fadar White House, Jami'an lafiya sun yi gargadin cewa babu mamaki mutanen da suka bar yankin a cikin 'yan kwanaki da suka gabata sun harbu da cutar.

    Gwamnan jihar, Andrew Cuomo, ya kwatanta yadda cutar ke bazuwa da 'jirgin kasa mai bala'in gudu', da yanzu hakan jiharsa tafi fuskantar barazana

  2. Sojojin Amurka sun kamu da coronavirus

    US Navy

    Asalin hoton, Getty Images

    A Karon farko, Sojojin ruwan Amurka uku sun harbu da coronavirus duk da cewa suna cikin jirgin ruwan yaki da ke kan teku.

    Tuni aka fara shirin kwashe su daga cikin jirgin da ke kan tekun Philippines, bayan wani gwaji da aka yi ya tabbatar suna dauke da kwayar wannan cuta.

    Wani jami'i a ma'aikatar tsaro ya shaida wa BBC cewa an killace dukkan ma'aikatan jirgi da suka yi mu'amala da mutanen da suka harbu da cutar.

    Wakilin BBC ya ce sai dai jami'in bai fadi komai kan adadin mutanen da ake kebe, amma ya ce jirgin na dauke da ma'aikata kusan dubu biyar a kan teku na phillipines.

    Kuma har yanzu ana nazarin yadda ma'aikatan suka samu wannan cutar.

  3. Coronavirus: Australia ta takaice yawan masu yin jana'iza idan an mutu

    Kasar Australia ta takaice yawan mutanen da ya kamata su yi wa 'yan uwansu jana'iza idan sun mutu sakamakon cutar coronavirus.

    Kasar dai ta kayyade cewa mutum 10 ne kawai aka yadda su halarci jana'iza sannan mutum biyar ne kacal aka amince da su halarci wurin bikin aure.

    Firai ministan, Scott Marrison ya bayyana wadannan matakan ne bayan fitowa daga wani zaman majalisar zartarwa.

    Har wa yau, kasar za ta haramta tafiye-tafiye zuwa kasashen waje sannan kuma za a rufe wuraren taruwar jama'a.

    Dokar dai wadda ta fara aiki a yau Laraba, na zuwa ne bayan kasar ta samu wadanda suka kamu da cutar 427 a awa 24.

    Yanzu haka akwai mutum 2,136 da suka kamu da coronavirus a Australia, inda kuma guda takwas suka mutu.

    Australia
  4. Coronavirus: 'Yan Najeriya 46 ne suka kamu ya zuwa yanzu - NCDC

    Hukumar takaita yaduwar cutuka ta Najeriya NCDC, ta ce an samu karin mutum 2 da suka kamu da coronavirus a kasar.

    Mutanen guda biyu da abin ya shafa daya a jihar Legas ya ke dayan kuma a jihar Osun.

    Dukkanin mutanen guda biyu dai sun koma kasar ne daga bulaguro a kasar waje a makon da ya gabata.

    NCDC ta wallafa hakan ne a safiyar ranar Laraba, inda ta ce adadin wadanda suka kamu da cutar ya zuwa karfe 7 na safiyar Larabar ya kai 46.

    Jihar Legas ce dai ta fi yawan wadanda suka kamu da cutar a Najeriya, sai kuma Abuja babban birnin tarayyar kasar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  5. Budewa

    Jama'a masu bibiyarmu barka da warka. Yaya muka ji da darurar annobar coronavirus? Allah ya takaita mana. Da fatan kuma za ku ci gaba da kasancewa da shafinmu na bbchausa.com domin kawo muku bayanai da dumi-duminsu dangane da cutar ta coronavirus. Mun gode.

  6. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka kawo karshen kawo muku labarai da rahotanni kai-tsaye.

    Sai kuma gobe Laraba idan Allah ya kaimu za mu ci gaba da kawo muku wasu sabbin labaran.

    Ku duba kasa domin karanta labaran da muka wallafa a yau musamman wadanda suka danganci coronavirus da ta zama annoba a fadin duniya.

    Mu kwana lafiya.....

  7. Za a rufe kasuwanni a Legas saboda coronavirus

    .

    Gwamnatin jihar Legas ta ce daga ranar Alhamis za a dakatar da duk wasu harkoki a kasuwanni da shaguna da kotuna da wuraren shakatawa a cikin jihar baki daya.

    Hakan dai na cikin matakan hana bazuwar cutar Coronavirus a cikin jihar.

    Gwamna Babajide Sanwo-Olu ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a jihar a ranar Talata inda ya ce matakan sun zama dole saboda ana kara samun karuwar adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya baki daya.

  8. Covid-19: An hana manyan motocin fasinja shiga Kano

    .

    Gwamnatin jihar Kano ta bayar da umarnin dakatar da manyan motocin daukar fasinja masu zuwa Kano daga Legas shiga jihar a yunkurin dakile yaduwar cutar coronavirus,

    Gwamnatin ta bayyana cewa ta haramta wa motocin kirar Luxurious shiga jihar sakamakon motocin na daukar mutane masu dimbim yawa wanda hakan zai iya sa wa a samu bullar cutar.

  9. Coronavirus: Tallafin biloniya dan China Jack Ma, ya iso Najeriya

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    A ranar Talata ne jirgin sama na dakon kaya na Ethiopia ya sauka a Legas a Najeriya, inda ya kawo kayan da wani hamshakin mai arziki dan kasar China kuma mamallakin Gidauniyar Jack Ma, ya bai wa nahiyar Afirka tallafi na amfanin asibiti da suka shafi cutar Covid-19.

    A ranar 16 ga watan Maris ne biloniya ya sanar da tallafin a shafinsa na Twitter, a yayin da kasashen duniya da dama ke ci gaba da fafutukar hana yaduwar cutar.

    Kayan sun hada da jaka 20,000 ga kowace kasa a Afirka wacce ta kunshi kayayyakin jinyar masu coronavirus da suka hada da takunkumin rufe fuska 100,000 da rigunan da ma'aikatan lafiya ke sa wa don kare kansu da sauran kayan da ake amfani da su wajen kula da masu cutar.

  10. An sake samun mutum biyu da ke dauke da coronavirus a Najeriya – NCDC

    Hukumar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC ta sake tabbatar da sake samun mutum biyu masu dauke da coronavirus a kasar.

    Kamar yadda ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce an samu mutum daya a Abuja daya kuma a jihar Bauchi.

    A halin yanzu mutanen da suka kamu da cutar a kasar sun kai 44 inda mutum biyu tuni suka warke sai kuma daya ya mutu.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  11. Labarai da dumi-dumi, Birtaniya na neman ma'aikatan agaji 250,000 saboda coronavirus

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakataren Lafiya na Birtaniya Matt Hancock ya bayyana cewa kasar na neman mutum 250,000 da za su bayar da agaji a fannin lafiyar kasar.

    Ya bayyana cewa masu bayar da agajin za su taimaka wajen sayen magunguna da kuma rarraba su ga wadanda aka killace saboda coronavirus.

  12. Labarai da dumi-dumi, Sojan Najeriya ya kamu da coronavirus

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Hedikwatar sojojin Najeriya ta tabbatar da cewa wani sojan kasar ya harbu da cutar numfashi ta coronavirus.

    Sojan, wanda matukin jirgin sama na yaki ne ya koma kasar ne daga wani bulaguron da ya yi zuwa kasar waje.

    Kwamanda Abdussalam Sani shi ne jami`in hulda da jama`a na cibiyar samar da bayanai a kan rundunoni na musamman na hedikwatar tsaron Najeriyar, kuma a tattaunawarsa da BBC ya ce a halin da ake ciki sojan yana jinya a asibiti

  13. Gwamnan Bauchi Bala Muhammad ya kamu da coronavirus

    Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya kamu da coronavirus bayan da sakamakon gwajinsa ya fito.

    A wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar mai dauke da sa hannun babban mai bai wa gwamnan shawara kan yada labarai Mukhtar M Gidado, a ranar Talata.

    BBC ta samu tabbacin haka daga wajen wani makusancin gwamnan.

    Sanarwar ta ce daga cikin mutum shida na jami'an gwamnatin Bauchin da aka yi wa gwajin, na gwamnan ne kawai ya nuna yana dauke da cutar.

    .

    Asalin hoton, BAUCHI STATE GOVERNMENT

  14. Iran ta ce ba ta bukatar agajin MSF kan coronavirus

    Kungiyar agaji ta Medecins San Frontier ta ce aikin jin kai da take bayarwa a Iran na cikin halin rashin tabbas.

    Wannan na zuwa ne bayan da ta samu bayanan cewa ta dakata da bayar da agajin wanda tuni ta fara gudanarwa.

    MSF ta ce ta bude wani asibitin wucin gadi mai gado 50 a garin Isfahan don ceto rayukan wadanda cutar Coronavirus ta yi wa mugun kamu.

    To amma wata jaridar Iran ta ruwaito cewa ministan lafiya ya dakatar da aikin MSF kuma ya ce gwamnati ba ta bukatar agaji daga waje a halin yanzu.

    Gwamnatin Iran ta sanar cewa mace-mace sanadiyyar cutar Covid-19 a yanzu ya kai mutun 1,900.

  15. Za a saka dokar hana fita a fadin Indiya saboda coronavirus

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Firai Ministan Indiya Narendra Modi ya bayyana cewa za a saka dokar hana fita a fadin kasar Indiya na tsawon kwanaki 21.

    Ya bayyana cewa dokar za ta fara aiki ne da misalin karfe 12:00 na dare.

    Indiya ce kasa ta biyu a yawan jama'a a duniya kuma a yanzu haka an samu mutum 482 da ke dauke da coronavirus, mutum tara kuma sun mutu.

  16. Amurka na iya zama cibiyar annobar coronavirus

    Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta yi gargadin cewa Amurka na iya zama cibiyar annobar coronavirus ta Duniya.

    A lokacin da take magana a Geneva, kakakin WHO Margaret Harris ta ce an samu karuwar masu dauke da cutar a kasar.

    “Ba za mu iya cewa ta zama ba tukun, amma akwai yiwuwar ta zama cibiyar annobar” kamar yadda ta shaida wa manema labarai, a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters.

    Kawo yanzu dai, an samu fiye da mutum 46,000 da cutar a Amurka kuma mutum 593 sun mutu, kamar yadda alkaluman jami’ar Johns Hopkins suka nuna.

    A yanzu dai Turai ce cibiyar annobar, inda Italiya ta fi ko wace kasa yawan mace-mace a nahiyar.

  17. Labarai da dumi-dumi, Coronavirus ta kashe mutum na farko a Saudiyya

    .

    Asalin hoton, AFP

    Saudiyya ta tabbatar da mutum na farko da ya mutu a kasar sakamakon coronavirus.

    Ma'aikatar lafiya ta kasar ta shaida cewa wanda cutar ta kashe dan asalin kasar Afghanistan ne kuma mai shekaru 51.

    Saudiyya ita ce kasar da ta fi yawan masu cutar a Gabas ta Tsakiya bayan Iran.

    A ranar Talata an samu karin masu dauke da cutar da mutum 205 inda yawansu a halin yanzu ya kai 767.

    Kasar ta saka tsatsauran matakai ciki har da dokar hana fita ta makonni uku domin kokarin dakile yaduwar cutar.

  18. Abba Kyari ya kamu da cutar coronavirus - Reuters

    Abba Kyari

    Asalin hoton, Presidency

    Shugaban ma'aikata a fadar shugaban Najeriya, Abba Kyari ya kamu da coronavirus kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya wallafa.

    Har wa yau, wata majiya mai tushe a fadar gwamnatin ta Najeriya, ta tabbatar wa da BBC labarin cewa " da gaske ne batun Abba kyari ya kamu da coronavirus."

    Kafin nan dai BBC ta nemi jin ta bakin mai magana da yawun shugaban kasa, Malam Garba Shehu kan al'amarin amma hakarta ba ta cimma ruwa ba.

    Reuters dai ta rawaito cewa Abba Kyari ya yi bulaguro zuwa Jamus a farkon watan Maris tare da wata tawagar jami'an gwamnatin kasar domin yin wani taro da kamfanin Siemens.

    Sai dai kamfanin na Reuters din ya ce babu tabbas ko Abba Kyari ya killace kansa ko a'a.

  19. An rufe makarantun allo da islamiyya a Bauchi

    Gwamnatin jihar Bauchi ta bi sahun wasu jihohin Najeriya na rufe makarantu inda ta rufe makarantun allo da islamiyya a fadin jihar.

    Dama tuni gwamnatin ta bayar da umarnin rufe makarantun boko a jihar.

    A wata sanarwa da kwamishinan ilimi na jihar Dakta Aliyu Tilde ya fitar, ya bayyana cewa su ma alamajirai na cikin hadari sakamakon suna bi kwararo-kwararo suna bara a gidaje domin neman abinci.

    Ya umarci masu makarantun allo da su mayar da almajiransu gida har sai an samu saukin wannan annoba

    ..

    Asalin hoton, Dr Aliyu Tilde

  20. Labarai da dumi-dumi, Covid-19: An samu karin mutum biyu da suka kamu a Najeriya

    Hukumar takaita yaduwar cututtuka ta Najeriya, NCDC ta ce an samu karin mutum biyu da suka harbu da cutar coronavirus a kasar.

    Mutanen guda biyu dai sun fito ne daga jihar Legas da Ogun.

    Daya daga cikin mutanen ya koma kasar ne daga tafiyar da ya yi kasar waje.

    Shi kuma mutum na biyu ya samu cutar ne bayan haduwa da wani wanda cutar ta harba.

    Hukumar ta ce alkaluman da suka samu a ranar Litinin karfe 1 na rana sun nuna 'yan kasar guda 42 ne suka kamu.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X