Abubuwan da suka faru a Nigeria da sassan duniya kan coronavirus

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma wasu sassan duniya, musamman rahotanni kan annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Gwamnatin Kano na feshin magani kan coronavirus

    Gamna Abdullahi Ganduje

    Asalin hoton, KNSG

    Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da shirin feshin magani a birnin baki daya tare da hadin gwiwar kamfanin Lee Group of Companies, a wani yunkuri na dakile cutar coronavirus.

    Yayin da yake kaddamar da shirin a harabar gidan gwamnati, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ce sun kaddamar da shirin ne albarkacin Ranar Tsafta ta kowace Asabar din karshen wata.

    "Wannan wani yunkuri ne na tsaftace muhallinmnu. Muna yakar wannan annoba da duk abin da za mu iya. Saboda haka muke korarta daga muhallanmu kuma shi ya sa Ma'aikatar Muhalli ke da matukar muhimmanci a yanzu," Ganduje ya bayyana a wata sanarwa da mai magana da yawunsa Abba Anwar ya fitar ranar Asabar.

    Motar feshin magani a Kano

    Asalin hoton, KNSG

    Ganduje ya ce aikin tsaftace birnin zai kai ga kasuwanni da asibitoci da sauran wuraren taruwar jama'a.

    Masu aikin tsaftace birnin sun fara da gidan gwamnati ne sannan suka wuce zuwa asibitin Muhammadu Abdullahi Wase (asibitin Nassarawa), inda gwamnan ya sanya ido kan aikin tare da wasu kwamishinoninsa.

    Gwamna Ganduje ya kara da cewa dalilin da ya sa rufe iyakokin Kano bai shafi wasu muhimman abubuwa ba kamar kayan abinci shi ne, domin kar a gurgunta harkar kasuwancin jihar.

    "Saboda kada mu gurgunta tattalin arzikin Kano, shi ya sa ba mu hana harkar kayan amfanin gaggawa ba irinsu abinci...Duk da cewa kasuwanni za su ci gaba da kasancewa a bude, muna kira ga mutane da su yi aiki da shawarwarin nesa-nesa da juna da kuma zama a gida."

  2. Wadanda ke warkewa daga coronavirus na karuwa a Spain

    A wani labari mai dadi, adadin mutanen da suke warkewa daga cutar Covid-19 a kasar Spain na karuwa.

    Wasu karin mutum 2,928 sun warke daga cutar, abin da ya kai jumullar adadin zuwa 12,285 - karin kashi 31 cikin 100.

    Kamar yadda rahotanni suka nuna, mutanen da suka mutu a kasar sun zarta 5,600, karin kashi 17 cikin 100 ke nan a cikin awa 24 kacal.

    Kazalika, wadanda suka kamu sun kai 72,248 daga 64,059 da aka bayar ranar Juma'a, karin kashi 12.8 cikin 100 kenan.

  3. Buhari ya gana da ministan lafiya kan coronavirus

    .

    Asalin hoton, @BashirAhmaad

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya tattauna da ministan lafiya na kasar Osagie Ehanire da kuma daraktan hukumar yaki da yaduwar cutuka ta kasar Chikwe Ihekweazu.

    Mai taimaka wa shugaban kasar kan kafofin sadarwa na zamani Bashir Ahmed ne ya wallafa a shafinsa na Twitter, inda ya ce shugaban ya karbe su ne a yau Asabar domin jin bayanai daga gare su kan yaki da yaduwar coronavirus.

    A farkon makon nan ne dai Abba Kyari, shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, ya kamu da coronavirus.

    Rahotanni sun ce gwaji ya nuna Buhari ba ya dauke da cutar. Kazalika, akwai 'yarsa guda daya da take killace tun a makon da ya gabata bayan ta dawo Najeriya daga birnin Landan.

    .

    Asalin hoton, @BashirAhmaad

    .

    Asalin hoton, @BashirAhmaad

  4. Matakai na baya-bayan nan kan coronavirus

    Kasashe da dama a fadin duniya na kara tsaurara matakai domin dakile yaduwar coronavirus.

    Wasu kasashen kan sa ka'idoji kadan wasu kuma sukan tsaurara inda har ake rufe kasa baki daya.

    Ga wasu daga cikin matakai na baya-bayan nan da aka kara tsaurarawa a wasu kasashe.

    -Ireland ta shiga mako na biyu kenan karkashin dokar hana fita inda aka tursasa kowa sai ya zauna a gida sai dai idan mutum na da wani muhimmin abin yi kamar neman abinci ko magani ko takaitaccen motsa jiki.

    'Yan sandan kasar ne ke tabbatar da cewa an bi dokar da aka saka.

    - An bukaci dattawa wadanda suka wuce shekaru 65 da kuma wadanda ba su da isassar lafiya su zauna a gida a kasar Malta.

    Wannan dokar ta shafi har da mata masu ciki, amma za su iya fita zuwa ganin likita ko samo abinci ko kuma wani babban uzuri.

    - A kasar Hungary kuma, an yarda jama'a su je wajen aiki da sauran hidimominsu na yau da kullum, sai dai ba a yarda da taron mutane a wuri guda ba.

    -Kasar Finland kuma ta takaita zirga-zirga a lardin Uusimaa, ciki har da babban birnin kasar wato Helsinki.

    Lardin ne ke da akasarin masu dauke da cutar coronavirus a fadin kasar.

  5. 'Mutum 39,000 za su iya kamuwa da coronavirus a Legas'

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Kwamishinan lafiya na jihar Legas a Najeriya Akin Abayomi ya bayyana cewa lissafi ya nuna cewa za a iya samun mutum 39,000 da za su iya kamuwa da coronavirus a jihar Legas.

    Kamar yadda jaridar The Nation ta kasar ta ruwaito, kwamishinan ya shaida cewa akwai yiwuwar mutanen da cutar za ta yi wa illa ba za su wuce 13,000 , ''amma hakan zai yiwu ne kadai idan jama'a sun bi ka'idar bayar da tazara tsakanin juna'' inji kwamishinan.

    Kwamishinan ya ce yawan mutanen da ya bayyana za su kamu kan iya firgitarwa, amma ya zama dole a kara tuni kan cewa a bi umarnin da aka bayar na kiyaye yaduwar wannan cuta.

  6. Wani mai shekara 101 ya warke daga coronavirus

    A yayin da ake samun mace-mace a Italy sakamakon annobar coronavirus, an samu wani mai shekara 101 da aka sallama daga asibiti saboda ya warke daga cutar.

    Mataimakiyar magajin garin Rimini da ke arewa maso gabashiun kasar ta shaida cewa wannan abin mamaki ne kuma hakan ya nuna cewa akwai rabo na alheri a nan gaba.

    A makon da ya gabata ne dai aka kwantar da shi asibiti bayan an masa gwaji an gano yana dauke da Covid-19.

    .

    Asalin hoton, Getty Images

  7. Jakadan Najeriya a Jamus da ya gana da Abba Kyari ‘ba ya dauke da coronavirus’

    .

    Asalin hoton, @YusufTuggar

    A wata sanarwa da jakadan Najeriya a Jamus Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya bayyana cewa ya tabbatar ba shi dauke da cutar coronavirus bayan ya karbi sakamakon gwajinsa a safiyar yau.

    “Na san wasu daga cikinku sun ga labarin da ke cewa ina tare da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Abba Kyari da gwamnan Bauchi Bala Mohd a Jamus kuma watakila ni ma ina dauke da cutar ko kuma dukkanmu mun harbu da cutar ne a can, in ji jakadan.

    Majiyoyi a fadar shugaban Najeriya ta Aso Rock da ke Abuja da dama dai sun tabbatar da cewa sakamakon gwajin cutar da aka yi wa Malam Abba Kyari ya nuna cewa ya harbu da cutar numfashi ta coronavirus.

    Haka zalika Bala Mohammed ya tabbatar da shi ma yana dauke da cutar a halin yanzu.

    Rahotanni sun ce shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasar ya je kasar ta Jamus ne a farkon watan Maris inda ake zargi a can ya dauko coronavirus.

    Jamus na cikin kasashen da cutar ta fi yi wa illa inda dukkan ‘yan kasar suka kamu da ita, yayin da ta kashe da dama daga cikinsu.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  8. Labarai da dumi-dumi, Covid-19: Mutanen da suka mutu a Spain sun zarta 5,000

    .

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Sojojin kasar ne ke aikin feshi da goge-goge a asibitocin kasar da wasu wurare da ake kula da marasa lafiya.

    Yawan mutanen da suka mutu a Spain saboda coronavirus sun zarta 5,000 bayan an samu mutum 832 da suka mutu a sa'o'i 24 da suka gabata.

    Yawan mutanen da suka mutu a halin yanzu a kasar sun kai 5,690 inda kuma jumullar mutum 72,248 ke dauke da cutar a halin yanzu.

    Spain ce kasar da annobar coronavirus ta fi yi wa illa a fadin nahiyar Turai.

    An saka dokar ta baci a kasar kuma ana ganin dokar za ta kai har zuwa 12 ga watan Afrilu kafin a sassauta ta inda tuni shaguna da wuraren kasuwanci a kasar aka rufe su.

    Sojojin kasar ne ke aikin feshin magani da goge-goge a asibitocin kasar da wasu wurare da ake kula da marasa lafiya.

    Kamar sauran kasashen duniya, ma'aikatan lafiya na kuka dangane karancin kayayyakin aiki a kasar ta Spain

  9. Za a rufe biranen Accra da Kumasi saboda coronavirus

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Ghana Nana Akufo Addo ya sanar da rufe birane biyu mafi girma a kasar na tsawon mako biyu.

    Rufewar ta rabi da rabi za ta fara aiki a Accra, babban birnin kasar da kuma Kumasi daga karfe daya na ranar Litinin mai zuwa.

    Babu kuma tafiye-tafiye tsakanin birane ko ta mota ko jirgin sama sai dai idan ya zama dole.

    Amma rufewar ba ta shafi bankuna da masu sayar da abinci da gidajen mai ba.

    Masu motocin haya kuma za su rage yawan fasinjojin da suke dauka.

    A Ghana mutum 137 aka tabbatar sun kamu da coronavirus kuma hudu sun mutu.

  10. Labarai da dumi-dumi, Coronavirus ta fara lafawa a garin da ta samo asali

    An fara samun sauki a garin Wuhan na China inda a nan ne cutar Coronavirus ta fara bulla.

    Bayan watanni biyu da aka shafe a garin ba shiga ba fita, a halin yanzu ana bari a shiga garin amma kuma ba a bari a fita.

    Ana sa ran a mako mai zuwa za a fara bude shaguna domin ci gaba da kasuwanci.

    Tun a Disambar bara ne 'yan garin Wuhan da ke lardin Hubei suka fara kokawa da cewa suna fama da wata cuta mai kama da ciwon huhu wato pneumonia.

    A kalla mutum 3.299 suka mutu sakamakon wannan cuta a lardin Hubei da ke kasar China kamar yadda kididdigar Jami'ar John Hopkins ta bayyana.

    .

    Asalin hoton, AFP

  11. Budurwar 'Davido' mawakin Najeriya ta kamu da Coronavirus

    .

    Asalin hoton, @davidoofficial

    Shahararren mawakin nan dan Najeriya David Adeleke (Davido) ya ce budurwarsa Chioma Rowland ta kamu da cutar Coronavirus, kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Instagram a ranar Juma'a.

    Ya ce ko da suka dawo daga Amurka shi da budurwarsa ba su da wata alama ta cutar, amma daga baya da aka yi musu gwaji sai aka ga matarsa Chioma na dauke da cutar amma shi ba shi dauke da cutar.

    Ya ce shi ma zai killace kansa na kwanaki 14.

  12. Ina aka kwana kan batun riga-kafin coronavirus?

    Babbar tambayar da jama'a da dama a fadin duniya ke yi a kullum ita ce yaushe za a samu riga-kafin cutar coronavirus?

    Farfesa Sarah Gilbert, ita ce ke jagorantar tawagar likitocin da ke gudanar da bincike a jami'ar Oxford da ke Ingila kuma ta bayyana cewa a halin yanzu suna iyakar bakin kokarinsu domin gaggauta gano riga-kafin wannan cuta.

    Ta shaida wa BBC cewa hada riga-kafi na daukar lokaci, amma sakamakon yadda wannan annobar ke bazuwa kamar wutar daji, suna gaggawa wajen nemo riga-kafin amma duk da haka akwai matakan da ake bi domin kar a samu kuskure.

    Ta bayyana cewa jami'ar na kokarin samar da maganin riga-kafin mai yawan gaske idan har aka tabbatar da ingancin amfani da shi.

    .

    Asalin hoton, Getty Images

  13. Wadanda suka kamu da Coronavirus a Najeriya sun kai 81

    A halin yanzu, yawan wadanda suka kamu da coronavirus a Najeriya sun kai 81, kamar yadda hukumar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta Najeriya ta bayyana a ranar Juma'a da misalin karfe 11:55 na dare agogon Najeriya.

    Cikin wadanda suka kamu da cutar, mutum 3 sun warke mutum daya ya mutu.

    Ga jerin jihohin da cutar ta bulla da kuma yawan mutanen da cutar ta harba:

    Lagos- 52

    Abuja- 14

    Ogun- 3

    Ekiti- 1

    Oyo- 3

    Edo- 2

    Bauchi- 2

    Osun-1

    Rivers-1

    .

    Asalin hoton, NCDC

  14. Farawa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin barkanmu da wannan rana ta Asabar. A yau ma za mu ci gaba da kawo muku labarai da rahotanni kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya musamman kan labaran da suka shafi annobar coronavirus.

  15. Rufewa

    Toh masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka kawo karshen labarai da rahotannin da muke kawo muku kai tsaye musamman kan cutar coronavirus.

    Da fatan za ku kasance da mu gobe Asabar inda muke fatan dorawa daga inda muka tsaya.

    Kafin nan, ku na iya duba kasa domin karanta abubuwan da suka faru a Najeriya da sauran sassan duniya ranar Juma'a.

  16. Shugaba APC Adams Oshiomhole 'bai kamu da coronavirus ba'

    Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta ce sakamakon gwajin da aka yi wa shugabanta Adams Oshiomhole ya nuna cewa ba ya dauke da cutar coronavirus.

    Sanarwar da Mallam Lanre Issa-Onilu, mai magana da yawun jam'iyyar ya fitar ranar Juma'a ta ce an yi wa Mr Oshiomhole gwajin ne ranar Alhamis.

    "Sakamakon fargabar da aaka nuna cewa mai yiwuwa ya yi mu'amala da mutanen da ke dauke da coronavirus, Oshiomhole ya gabatar da kansa domin a yi masa gwaji ranar Alhamis kuma sakamakon gwajin ya nuna cewa ba ya dauke da cutar," in ji Mallam Lanre Issa-Onilu

    Oshiomhole

    Asalin hoton, APC

    Bayanan hoto, An yi wa Oshiomhole gwajin cutar ranar Alhamis
  17. Labarai da dumi-dumi, Karin mutum biyar sun kamu da coronavirus a Najeriya

    Hukumar yaki da yaduwar cutuka ta Najeriya, NCDC, ta ce an samu karin mutum biyar da suka kamu da cutar a kasar.

    A sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Juma'a, NCDC, ta ce uku daga cikinsu daga Abuja suke, yayin da biyu kuma daga Oyo suke.

    Jumulla mutum 70 ne kenan suka kamu da cutar ta coronavirus a kasar, yayin da mutum uku suka warke sannan mutum daya ya mutu.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  18. Coronavirus: Gwamnatin Kebbi za ta takaita zirga-zirga

    Gwamnatin jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya ta ce za ta takaita zirga-zirgar da ta hada da shiga da fita daga jihar saboda fargabar yaduwar coronavirus.

    Sanarwar da Abubaka Mu’azu Dakingari, mai magana da yawun gwamnatin jihar ya aike wa manema labarai ranar Juma'a, ta ce dokar takaita zirga-zirgar za ta soma aiki ne da daren ranar Asabar 28 ga watan Maris.

    Sanarwar ta ambato Gwamna Abubakar Atiku Bagudu yana bayar da umarnin a jawabin da ya yi ga al'ummar jihar ranar Juma'a.

    Ya kara da cewa dokar ba za ta shafi ma'aikatan gaggawa ba, irin su ma'aikatan lafiya da jami'an tsaro da masu kai magunguna da abinci da kuma gidajen sayar da man fetur.

    Gwamna Bagudu ya kuma bayar da umarnin rufe dukkan makarantu ciki har da na Islamiyya da na allo sai abin da hali ya yi.

    Gwamnan ya nada wani kwamitin da zai tabbatar da bin wannan umarni.

    Gwamna Bagudu

    Asalin hoton, Kebbi state government

    Bayanan hoto, Gwamnan ya nada wani kwamitin da zai tabbatar da bin wannan umarni.
  19. Yadda ake warkewa daga cutar coronavirus

    Mamayar da coronavirus ta yi wa kasashen duniya da kuma bayanan da masana kiwon lafiya ke yi kan yadda ake daukarta na cikin abubuwan da suka fi tayar wa da mutane hankali.

    Sai dai duk da cewa kusan mutum 600,000 ne suka kamu da cutar a duk fadin duniya yayin da sama da mutum 26,000 suka mutu sakamakon harbuwa da ita, akwai kuma fiye da mutum 128,000 da suka warke.

    Masana kiwon lafiya

    Asalin hoton, Getty Images

  20. Tarihin manyan annoba da suka shafi arewacin Najeriya

    Bullar annobar coronavirus a duniya a wannan karni da irin barnar da take yi suna tayar da hankulan jama'a da dama.

    Duniya ta jima ba ta ga wani lamari da ya rikita kowa ba, ya kuma jefa fargaba da rudu a duk sassan duniya kamar abin da coronavirus ko covid-19 ta haifar.

    Sai dai har yanzu a Najeriya dumbin mutane ne ke da shakku ko ma kin yarda da cewa cutar gaskiya ce.

    Ita ma annobar sankarau na daga cikin wadanda suka addabi al'ummar arewacin Najeriya

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Ita ma annobar sankarau na daga cikin wadanda suka addabi al'ummar arewacin Najeriya