Yadda ranar Juma'a ta kasance a nahiyar Asiya
Yadda ranar Juma'a ta kasance a nahiyar Asiya
- Hukumomin Koriya Ta Kudu na ta rokokn mutane da su zauna a gida bayan da aka samu karin mutum 91 masu dauke da cutar, lamarin da ya sa yawan masu ita ya kai 9,332. Firai Minista Chung Sye-kyun ya shaida wa maneman labarai cewa ya fahimci tun da bazara ta zo zai yi wa mutane wahala su yi ta zama a cikin gida ba fita, amma ya ba da shawarar cewa ''gara a yi hakuri a sha wahalar hakan maimakon a ci gaba da fuskantar barazanar wannan annoba har tsawon lokaci.''
- Firai Ministan Pakistan Imran Khan ya sanar da cewa zai kaddamar da wata tawaga ta matasa da ake kira Corona Relief Tigers, wadanda za su rarraba abinci ga mutanen da aka tursasa wa zama a gidajensu, a cewar wata jaridar kasar.
- An umarci mazauna Tokyo babban birnin Japan da su zauna a gida a karshen mako, hakan ya jawo an samu dogwayen layuka a shagunan sayar da kaya don mutane na rububin yin cefane. Gwamnan birnin Yuriko Koike ya yi gargadi cewar Tokyo na gab da fukantar tashin hankalin karuwar wadanda za su kamu da cutar
- Miliyoyn ma'aikatan kamfanoni a Bangladesh suna fuskantar barazanar yunwa bayan da masu sarin kayayyaki daga Turai da Amurka suka soke odar kayayyakin da suka yi, a cewar shugaban masu masana'antun yin kayayyaki a Bangladesh.























