Coronavirus: Jami'an tsaron Uganda na korar mutane daga tituna

Asalin hoton, Getty Images
Kasar Uganda ta sanar da samun karin masu dauke da coronavirus mutum hudu abin da ya kara yawan masu dauke da cutar zuwa 18.
Wannan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da gwamnatin kasar ta sa dokar kulle ta mako biyu, inda jami'an tsaro ke fatattakar duk wanda suka gani a waje.
Shugaba Yoweri Museveni ya ce an gano sabbin masu dauke da cutar da aka samu ne bayan an gudanar gwajin cutar a kan mutum 197 da suka koma kasar daga Dubai.
Yanzu haka dai harkokin kasuwa a Kampala, babban birnin kasar sun tsaya cak.
Ana fargabar cewa matalauta ka iya shiga wani hali sakamakon sai sun fita suke neman abin da za su saka a bakinsu bayan kuma gwamnati ba ta ba su tallafi ba.












