Kofin Carabao : Liverpool za ta yi wasan ƙarshe da Chelsea

Asalin hoton, Getty Images
Liverpool za ta kara da Chelsea a wasan karshe na cin Kofin Carabao bayan da ta yi nasarar fitar da Fulham daga gasar.
Kungiyar ta Anfield ta samu wannan nasara ne bayan da suka tashi kunnen doki - 1-1 a gidan Fulham, Craven Cottage, ranar Laraba da daddare, a wasansu na biyu.
Kasancewar a karawarsu ta farko a Anfield, Liverpool ta doke Fulham da ci 2-1, sakamakon ya kasance Reds din ta yi galaba da ci 3-2, wanda hakan ya sa za ta fafata a wasan na karshe a Wembley ranar 25 ga watan Fabrairu mai kamawa.
A karawar ta Laraba Luis Diaz ne ya ci wa Liverpool kwallonta a minti na 11, amma kuma Issa Diop ya farke wa mai masaukin bakin a minti na 76.
Dukkanin kungiyoyin biyu sun kai wasan zagaye na hudu a gasar cin kofin hukumar kwallon kafa ta Ingila, FA, inda a karshen makon nan Fulham za ta karbi bakuncin Newcastle a ranar Asabar, ita kuwa Liverpool za ta kasance a gida da Norwich ranar Lahadi.
Yanzu dai Fulham za ta ci gaba da neman damar ta ta farko ta kaiwa wasan karshena cin kofin na EFL a tarihi, da ba ta taba yi ba.
A ranar Talata ne Chelsea ta samu nasarar zuwa wasan na karshe bayan da ta doke Middlesbrough ta gasar kasa da Premier, wato Championship, wadda ta ci karawarsu ta farko 1-0.









