KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 19/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Taƙaitattu

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • Sadis Buba

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Yusuf Mohammed da Abdullahi Bello Diginza

  1. Tsoffin Janar-Janar sun yi kira da a ingata harkar tsaro bayan rasuwar Rabe Abubakar

    ...

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Tsoffin hafsoshin sojin Najeriya kuma abokan aikin marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar (rtd) sun yi kira da a yi wa tsarin tsaron Najeriya garambawul bayan rasuwar tsohon Janar ɗin a hannun wasu ƴan bindiga da suka sace shi a jihar Katsina.

    Sun yi wannan kira ne a ranar Alhamis ɗin da ta gabata yayin wani taron manema labarai a Kaduna wanda Birgediya Janar Isma’ila Abdullahi (rtd) ya yi magana a madadin abokan aiki da kuma makusantan marigayin.

    Da ya ke magana yayint aron Brig.-Janar Maharazu Tsiga (rtd), tsohon darakta-Janar na hukumar kula da masu yi wa ƙasa hidima (NYSC), ya yi kira da a ɗauki ƙwararan matakai don magance matsalar rashin tsaro a ƙasar.

    A cewar sa, ana buƙatar a ƙddamar da dabarun da za a bi don wargaza ayyukansu da kuma dawo da zaman lafiya.

    "Waɗannan mutane ƴan adam ne kamar mu; suna tsoron mutuwa kuma suna tsoron a fuskance su gaba da gaba. Idan muka kawar da tsoro ta a zukatan mu kuma muka fuskanci su da gaske, za mu sami sakamako mai ma'ana fiye da tattaunawar da babu ranar ƙarewa," in ji shi.

    Da yake bayanio kan lokacin da ya kwashe a hannun ƴan bindiga, Tsiga ya ce da wuya ƙungiyoyin ƴan ta'adda da yan bindiga su miƙa wuya bisa radin kansu ta hanyar tattaunawa.

  2. Bolivia ta ƙulla yarjejeniyar dala miliyan 20 da Amurka don yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi

    ...

    Asalin hoton, Cancillería Bolivia

    Bolivia ta ce ta rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya ta haɗin gwiwa da Amurka domin yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi.

    Ma'aikatar harkokin wajen ƙasar ta ce a ƙarƙashin yarjejeniyar, Amurka za ta samar da dala miliyan 20 (£15m) domin horas da sojojin Bolivia da kuma samar da kayan aiki a wani ɓangare na yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi.

    Yarjejeniyar dai ita ce alama ta baya-bayan nan da ke nuna yunƙurin farfado da dangantaka tsakanin kasashen - shekaru 18 bayan da shugaban ƙasar na wancan lokaci Evo Morales ya kori hukumar yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Amurka daga ƙasar, wadda ita ce ƙasa ta uku a duniya wajen samar da ganyen Coca da ake amfani da shi wajen haɗa hodar iblis.

    A ƙarkashin sabon shugaba Rodrigo Paz, Bolivia ta shiga wani shirin tsaro da Amurka ke jagoranta a yammacin duniya.

    A cikin wata sanarwa, ofishin jakadancin Amurka ya tabbatar da cewa "Amurka za ta yi aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin Bolivia domin ba da horo, da kayan aiki, da sauran nau'ukan tallafi".

  3. Amurka ta ɗage shingen sojojin ruwanta daga gaɓar tekun Iran

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Amurka ta janye shingen sojojin ruwa da ta kafa a gaɓar tekun Iran bayan da ƙasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin gabas ta tsakiya.

    Cibiyar gudanar da al'amuran tsaro na Amurka ta tabbatar da kawo ƙarshen takunkumin a shafin X "bisa ga umarnin shugaban ƙasa", kuma ta ce wasu jiragen ruwa na Amurka za su ci gaba da kasancewa "a wasu sassan yankin".

    Jim kaɗan bayan haka, Jagoran Addinin Musulunci na Iran Mojtaba Khamenei ya ce ya amince da yarjejeniyar da Amurka duk da cewa ra'ayinsa ya bambanta, ba tare da yin wani ƙarin haske ba.

    Ya ce ya amince da yarjejeniyar ce bayan da shugaban ƙasar Iran Masoud Pezeshkian ya ba da tabbacin cewa zai kare haƙƙin al'ummar ƙasar.

    Wannan shi ne karon farko da Khamenei ya yi tsokaci kan yarjejeniyar.

    Bai fito bainar jama'a ba tun bayan hawansa karagar mulki a watan Maris ɗin da ya gabata bayan kisan mahaifinsa kuma magabacinsa Ayatullah Ali Khamenei a harin da Amurka da Isra'ila suka kai wa Iran a ranar 28 ga watan Fabrairu wanda ya haifar da yaƙin.

  4. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Ibrahim Yusuf Mohammed da Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniyar ke ciki.

    Za ka iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta.