An hana kungiyoyin Iran buga wasannin AFC Champions League a cikin kasar

Persepolis

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, 'Yan wasan Persepolis suna murna bayan cin kwallo a gasar AFC Champions League
An wallafa

Kungiyoyi hudu na kwallon kafa a kasar Iran da ke buga gasar Zakarun Asiya ta AFC Champions League sun ce ba za su buga wasannin gasar ba idan har ba za su karbi bakuncin wasannin ba, a cewar rahoton kamfanin dillancin labarai na Mehr.

Hukumar kwallon kafar Iran ta ce hukumar AFC ta hana kungiyoyin Iran buga wasanninsu na gida a cikin Iran.

AFC ta ce tana son wasannin da kungiyoyin za su yi a buga su a wajen kasar.

Wannan yunkurin ya zo ne yayin da dangantaka take kara tsami tsakanin Iran da Amurka.

Hukumar kwallon kafar Iran ta ce za ta sanar da "matsayarta" a cikin 'yan kwanaki "masu zuwa".

Iran tana da kulob hudu a gasar AFC Champions League - Persepolis da Esteghlal da Sepahan da Shahr Khodro kuma a yau Asabar ake sa ran za a tuntube su.

Sai dai Mehr ya ce kungiyoyin za su mika wasika ga AFC domin bayyana cewa za su fice daga gasar idan ba za su buga wasan gida a Iran ba.