Macron na son Najeriya ta goyi bayan Faransa a Rasha

Emmanuel Macron

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ya nemi 'yan Najeriya su goyi bayan kasarsa a gasar kofin duniyar da ake yi a Rasha.

Shugaban ya yi wannan maganar ne a lokacin da ya kai ziyara Najeriya.

Macron ya ce "tun da dai Najeriya ta fice daga gasar kamata ya yi 'yan kasar su mara wa kasarsa baya."

Wakilin sashen wasanni na BBC, Nick Cavell, ya ce 13 daga cikin 'yan wasan dake tawagar Faransa za su iya taka wa wata kasar Afirka leda.

Dan uwan Paul Pogba, Florentin, yana buga wa Guinea ( ya kuma buga wa 'yan kasa da shekara 20 na Faransa wasa)

Dan uwan Steve Mandanda, Parfait, yana buga wa Jamhuriyar Dimkradiyyar Kongo wasa (kuma ya buga wa tawagar 'yan kasa da shekara 21 ta Faransa wasa).

A wasanta na gaba, Faransa za ta kara ne da Uruguay ranar Juma'a zagayen kusa da dab da karshe.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X