Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yadda aka gudanar da zaben gwamnoni a Najeriya

Wannan shafi ne da ke kawo rahotanni da bayanai da kuma sharhi kan yadda aka gudanar da zaben gwamnoni da na 'yan majalisar jihohi a Najeriya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita, Mohammed Abdu and Awwal Ahmad Janyau

  1. Bidiyon Tambuwal a yayin da yake jefa kuri'arsa

  2. Za a fara kidaya kuri'u a Benue

    Ana shirye-shiryen fara kidaya kuri'u a rumfar zaben gidan gwamnatin jihar Benue.

  3. Atiku Abubakar ya kada kuri'a

    Dan takarar shugabancin Najeriya a karkashin jam'iyyar PDP a zaben 2019, Atiku Abubakar, ya kada kuri'arsa a garin Yola na jihar Adamawa ranar Asabar.

  4. An fara kidaya kuri'u a Kano

    An fara kidaya kuri'u a wata mazabar da ke unguwar Shagari Quarters a jihar Kano, kamar yadda wakilinmu Mansur Abubakar ya tabbatar mana.

  5. Abba Kabir Yusuf ya kada kuri'arsa

    Dan takarar jam'iyyar PDP a Kano Abba Kabir Yusuf ya kada kuri'arsa a Kano.

  6. Ba kasuwa ga masu talla a rumfunan zabe a Abuja

    Zaben shugaban kasa da aka gudanar a Najeriya na 23 na shugaban kasa ya sha bamban da na gwamnoni da na 'yan majalisar jihohi da ake yi a halin yanzu.

    A wannan karon an samu karancin fitowar jama'a a birnin tarayyar Najeriya Abuja inda ake zaben kananan hukumomi.

    Masu sana'o'i daban-daban na kokawa kan yadda suka fito da kayan talla amma ba kasuwa.

  7. Rumfar zabe a fadar shugaban kasa

    An samu karancin fitowar mutane a rumfunan zabe a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  8. Wani mai bukata ta musamman a rumfar zabe

    Wani mai bukata ta musamman kenan mai suna Atsen Azi a rumfar zaben Zarazo da ke karamar Hukumar Jos ta Gabas.

  9. Yadda ake cinikin gurasa a rumfar zabe

    Bidiyon yadda mai sayar da gurasa ke sana'arsa a wata rumfar zabe a Kano.

  10. Tambuwal ya kada kuri'arsa

  11. Mata na sassaka a Gezawa a jihar Kano

  12. Masallatai na kira a fito zabe a Jos

    Masallatai a Dogon karfe da ke Jos sun yi amfani da lasifikarsu domin kiran mutane a fito a kada kuri'a.

    Sun yi hakan ne sakamakon karancin fitowar mutanen da aka samu a ranar zabe.

    Rahotanni dai sun bayyana cewa bayan kiran da masallatan suka yi, jama'a da dama sun yiu tururuwa domin zuwa rumfunan zabe su kada kuri'arsu.

  13. Yadda wasu ke hidimarsu a ranar zabe a Legas

  14. Saraki ya kada kuri'arsa

    Shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki ya kada kuri'arsa a rumfar zabe mai lamba 005/006 da ke Agbaji a karamar hukumar Ilorin ta yamma a jihar.

  15. Bola Tinubu ya kada kuri'a

    Tsohon gwamnan Legas kuma jigo a jam'iyyar APC Bola Tinubu ya kada kuri'a.

  16. Wamakko ya kada kuri'arsa

    Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma jigo a jam'iyyar APC Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko kenan a lokacin da ya ke kada kuri'arsa.

  17. Yadda Sanwo-Olu ya kada kuri'arsa

    Dan takarar gwamna a jihar Legas na jam'iyyar APC, Babajide Sanwo-Olu a lokacin da yake kada kuri'arsa.

  18. Jonathan da Patience sun kada kuri'unsu

    Tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan da matarsa Patience sun kada kuri'a a mazabar Otuoke da ke jihar Bayelsa.

  19. Bidiyon yadda EFCC ta kama makudan kudade a jihar Benue

  20. Bidiyon yadda Buhari ya kada kuri'arsa

    Shugaban Najeriya kenan Muhammadu Buhari a yayin da yake kada kur'arsa a mazabarsa da ke Kofar Baru a Daura