An fara karbar sakamako a jihar Bauchi
- Marubuci, Ishaq Khalid
- Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Africa, Abuja
An soma karbar sakamako. Karamar hukuma ta farko ita ce Bogoro.
A jawabinsa gabanin soma karbar sakamako, Kwamishinan hukumar zabe a jihar Bauchi, Alhaji Ibrahim Abdullahi, ya bukaci wadanda suka samu nasara da wadanda suka fadi da magoya bayansu da su nuna sanin ya kamata kuma su kiyaye doka bayan bayyana sakamakon. ‘Masu nasara su nuna karimci, wadan da suka fadi su nuna juriya”, in ji shi.
Ya kara da cewa a ganinsu wannan zabe na daga cikin wadan da aka fi samun nasara da kwanciyar hankali wajen gudanar da shi.