Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yadda aka gudanar da zaben gwamnoni a Najeriya

Wannan shafi ne da ke kawo rahotanni da bayanai da kuma sharhi kan yadda aka gudanar da zaben gwamnoni da na 'yan majalisar jihohi a Najeriya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita, Mohammed Abdu and Awwal Ahmad Janyau

  1. An tsaurara tsaro a jihar Bauchi

      • Marubuci, Ishaq Khalid
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Africa, Abuja

    An tsaurara matakam tsaro a kewayen ofishin hukumar zabe ta kasa dake jihar Bauchi, yayin da ake jiran sakamakon zaben gwamna daga kananan hukumomin jihar 20 bayan da jama’a suka kada kuri’a ranar Asabar.

  2. An kai sakamakon zaben kananan hukumomi 10 na Kano

    A jihar Kano jami'an zabe sun ce an kai sakamakon zaben kananan hukumomi 10 daga 44 da ke jihar a zaben gwamna da majalisa.

  3. Muna kawo muku labarai kai tsare a radiyo

    Kuna iya sauraren labaran da muke kawo muku kai tsaye a radiyo , za kuma ku iya kallon shirin kai tsaye a BBC Hausa Facebook.

  4. Za a ci gaba da zabe a wasu wurare a jihar Kogi

    A jihar Kogi hukumar 'yan sanda ta tabbatar da kashe mutum biyu a karamar hukumar Ankpa, da kuma kona gidaje a wani kauye, a lokacin gudanar da zaben 'yan majalisar jiha a jiya Asabar.

    Sai dai hukumar ta ce a shirye take wajen ganin ta tabbatar an gudanar da zabe cikin lumana a yankuna da aka dage zabe zuwa yau Lahadi.

  5. Ana tattara sakamakon zaben Najeriya da aka yi ranar Asabar

      • Marubuci, Muhammad Annur Muhammad
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC africa, Abuja

    Tun a ranar Asabar aka fara tattara kuri'u, a zaben gwamnoni da na 'yan majalisar jihohin Najeriya da aka yi ranar Asabar.

    Tun da misalin karfe biyu na ranar ne dai aka rufe kada kuri'u a rumfunan zabe a hukumance. Sai dai an samu karancin fitowar masu kada kuri'u a zaben a wurare da dama, ciki har da babban birnin kasar Abuja.

    Haka kuma an samu zarge-zarge na sayen kuri'u a lokacin zaben.

    Zaben shugaban karamar hukuma da na 'yan kansuloli aka gudanar a Abuja.

  6. Za a fara tattara sakamakon zabe a Kano

      • Marubuci, Mansur Abubakar
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Pidgin, Kano

    Jami'in hukumar zabe a jihar Kano, Garba Lawan ya shaida wa BBC cewa za a fara karbar sakamakon zaben gwamna ranar Lahadi da karfe 9:00 na safe agogon Najeriya.

  7. EFCC ta kama dan takarar majalisa da tarin kudi

    Hukumar hana cin hanci da zagon kasa ta Najeriya, EFCC ta kama dan takarar majalisar dokoki na jihar Ogun, Sotayo Olatayo Johnson.

    Hukumnar ta kama Johnson da tarin kudi da suka kai N1,709,000 wadan da aka shirya a ambulan da dama sannan aka sa a cikin jaka.

    An kama dan takarar ne a mazabar Ijaye da ke birnin Abeokuta a jihar Ogun.

  8. Barkanmu da safiya

    Barkanmu da saduwa a shirin yadda aka yi zaben gwamnoni da na 'yan majalisa a jihohin Nigeria.

    An kammala zaben tun a ranar Asabar, inda ake tattara sakamako domin bayyana wadan da suka yi nasara.

    Za ku iya bibiyar shirin kai tsaye a BBC Hausa Facebook ko ta Tuwita ko kuma ta Instagram duk a BBC Hausa.com

  9. Sai gobe, Zaben gwamnoni da 'yan majalisar jiha a Najeriya

    A nan za mu dakata da kawo rahotanni da bayanai kai tsaye, sai kuma gobe idan Allah ya kai mu inda za mu ci gaba da kawo bayanai kan sakamakon zaben gwamnoni da aka gudanar a ranar Asabar.

    Da fatan za ku ci gaba da kasancewa da mu.

  10. Ana shirin fara tattara sakamakon zaben jihar Rivers

    Zauren da za a fara tattara sakamakon zaben jihar Rivers da ke kudancin Najeriya ta fara daukar harami.

  11. 'Yan sanda sun yi hadarin mota yayin aikin zabe

    Babban sufeton 'yan sandan Najeriya Mohammed Adamu lokacin da ya je asibitin unguwar Area 1 a Abuja, don duba wasu jami'an hukumar da suka yi hadarin mota a kan hanyarsu ta fara aikin zabe ranar Juma'a.

  12. Wasu daga cikin ma'aikatan BBC a bakin aiki

  13. Gwamnan Bauchi ya sha kaye a rumfarsa

    Gwamnan Bauchi Muhammad Abdullahi Abubakar ya fadi rumfarsa inda jam'iyyar APC ta samu kuri'u APC 288 sai kuma jami'iyyar PDP ta samu kuri'u 358.

  14. Labarai da dumi-dumi, An kashe mutane biyu a jihar Ribas

    An kashe mutane biyu a Akinma dake yammacin Ahoada da ke jihar Ribas.

    Wani da ya shaida lamarin ya shaidawa BBC cewa 'yan daba sun soki wani da kwalba a kirji inda ya mutu nan ta ke.

    A wani bangaren kuma aka harbi wani a kafa inda daga baya ya mutu a asibiti.

    Ahoada ta yamma dai na daya daga cikin wuraren da ba a kammala zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar tarayya ba sakamakon rikicin da ya barke.

  15. Labarai da dumi-dumi, An kama mota makare da kuri'u a Kano

    Jami'an 'yan sanda a Kano sun tabbatar da kama wata mota makare da kuri'u a unguwar Magwan da ke Kano kusa da gidan mataimakin gwamnan jihar.

    A yanzu haka 'yan sanda a jihar na bincike a kan lamarin.

  16. Labarai da dumi-dumi, INEC za ta sake sabon zabe a Benue

    Hukumar INEC ta ce za ta gudanar da sabon zabe a kananan hukumomi hudu a Benue sakamakon 'yan daba da suka kwace kayan zabe a yankin.

    Kananan hukumomin sun hada da Logo da Gwer ta gabas da Takar da kuma Gboko.

    Shugaban INEC a jihar ya Nentawe Yilwada ya bayyana cewa a yanzu haka 'yan sanda na bincike a kan wannan lamarin.

  17. Ra'ayoyi daga shafin Twitter

  18. Yadda ake sayen kuri'u

  19. Ra'ayoyi daga shafin Twitter

  20. Yadda gidan mai ya zama rumfar zabe a Legas

    Wani gidan mai kenan da ya zama rumfar zabe a Ikeja dake jihar Legas. Wannan ce rumfa mai lamba 23 a mazaba ta 3 da ke Ikeja.