Mai shekara 90 ta yi shirin zabe a Gayam
Gado mai shekara 90 na shirin yin zabe a Gayam Lafiya, Nasarawa

Wannan shafi na kawo muku yadda jama'a ke bayyana murna kan lashe zaben Najeria da shugaba Muhammadu Buhari ya yi.
Awwal Ahmad Janyau and Mohammed Abdu
Gado mai shekara 90 na shirin yin zabe a Gayam Lafiya, Nasarawa

Wasu na jiran kada kuri'a a mazabar Gayam da ke birnin Lafiya na jihar Nasarawa.



Asalin hoton, bbc
Hotuna sun nuna yadda Shugaba Muhammadu Buhari ya kada kuri'a inda ya zabi kansa.
Mai daukar hoto na kamfanin dillancin labaran Reuters ya dauki hotunan takardun kada kuri'ar Buhari, wadanda suka nuna cewa ya zabi kansa.
Hukumar zaben Najeriya dai tana ba da shawara kada masu kada kuri'a su bayyana wanda suka zaba, saboda hakan ya saba tsarin tarbiyyar dimokradiyya.

Asalin hoton, Reuters

Asalin hoton, Reuters
Masu zabe sun yi layi a mazabar makarantar firamare da ke Utako a Abuja, babban birnin Najeriya.



Wani dattijo da aka bai wa wajen zama domin kada kuri'a a mazabar dan takarar shugaban Najeriya a jam'iyyar PDP Atiku Abubakar da ke Yola, Adamawa.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce shi ne zai lashe zaben Najeriya.
Da yake amsa tambayar da wakilin BBC ya yi masa kan ko zai amince idan ya sha kaye, sai ya ce "Zan taya kaina murna" saboda ni zan ci zabe.

Mutane sun kaurace wa titunan Makurdi, babban birnin jihar Benue sakamakon zabukan da ake gudanarwa a duk fadin Najeriya.




Wannan hoton wani akwatin da ke dauke da katunan zabe da aka samu sun lalace a kwalejin Rumfa da ke jihar Kano da ke arewacin Najeriya.

Abdullahi Musa mai sanaar faci a garin Bodinga da ke jihar Sokoto ya ce ba zai yi zabe ba.

Masu kada kuri'a sun fito a Dutsen Alhaji da ke Abuja.Tun da sanyin safiya mutane suka hau layi.



'Yan Najeriya mazauna Amurka sun taya Najeriya murnar gudanar da manyan zabuka, inda suka yi addu'ar samun shugabanni na gari.
Masu zabe sun yi layi a birnin Abuja domin kada kuri'unsu a babban zaben Najeriya.

Mazabar Ajiya mai lamba 012 da ke Arewacin Yola, wurin da dan takarar shugaban kasa jam'iyar PDP, Atiku Abubakar.


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mai dakinsa Aisha Buhari sun kada kuri'unsu a mazabarsa da ke garin Daura na jihar Katsina.
Wakilan hukumar zabe sun isa Ajiya Dan Nabara, mazabar Ajiya da ke Arewa cin Yola, jihar Adamawa..


Masu kada kuri'a na jiran kayan zabe a rukunin gidaje da ke Shagari Quaters da Kundila a kwaryar birnin Kano.





Mun zabo wasu daga cikin ra'ayoyin da kuka bayyana game da zaben Najeriya a shafinmu na Facebook. Ga wasu daga cikinsu:
Lawal S Zazzau Hakila yau ce ranar da mu 'yan Nigeria za mu kada kuri'unmu domin yanzu haka ma ni har na hau kan layi ina jira a kawo kayan zabe domin na jefa kuri'a ta ga wanda nake so.
Abubakar Kawu Girgir Babu shakka mun shirya tsaf domin yanzu haka muna kan layin zabe domin yin tankade da rairaya a tsakanin 'yan takaarar da suka tsaya neman kujeru daban-daban.
Jamilu Musa Sabonlayi Hakika rana ba ta karya domin haka na shirya tsaf domin fita kada kuri'a ta.
Nura Lawali Danda Mu al'ummar jahar Zamfara mun shirya sosai domin kada kuri'unmu ga wanda muke so.
Masu hayar mota na ci gaba da harkokinsu a birnin Owerri da ke jihar Imo. Da alama neman kudi suka sanya a gaba ranar zabe.


Mutane da dama ne suke tsere wa daga Geidam na jihar Yobe da ke arewa maso gabashin Najeriya sakamakon harbe-harebn da ake ji daga ko wanne bangare na garin. Bayanai sun ce manyan motoci sama da 200 ne dauke da mutane suka fice daga garin