Buhari ya yi kwaskwarima a majalisar ministocinsa

Shugaba Muhammadu Buhari

Asalin hoton, Nigeria Presidency

Bayanan hoto, A watan Agusta ne Buhari ya rantsar da majalisar ministocinsa
An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya yi garambawul ga majalisar ministocinsa kasa da wata biyu bayan rantsar da su.

Garambawul din ya shafi musayar ma'aikata ne tsakanin Karamin Ministan Neja Delta Festus Keyamo da kuma Senator Tayo Alasoadura shi ma karamin minista a Ma'aikatar Kwadago.

Mista Keyamo ne zai koma Ma'aikatar Kwadagon, inda shi kuma Senator Alasoadura zai koma ta Niger Delta, dukkaninsu a matsayin kananan ministoci.

Wannan bayani na kunshe ne a wata sanarwa da daraktan yada labarai na ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha ya fitar.

Willie Bassey ya ce wannan sauyi zai fara aiki ne nan take wato ranar Talata 24 ga watan Satumbar 2019.

Tuni Festus Keyamo ya gode wa shugaban kuma har ya halarci sabuwar ma'aikatar tasa, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Twitter.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X