An gano maganin hana coronavirus yaduwa

Wannan shafin na kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma sauran kasashen duniya har da rahotanni kan coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Ba ni da hannu a cire Sarki Sanusi II – Buhari

    .

    Asalin hoton, Nigeria Presidency

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa bai da hannu a tsige Tsohon Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.

    Mai magana da yawun shugaban kasar Malam Garba Shehu ne ya wallafa haka a shafinsa na Twitter inda ya bayyana cewa duka maganganun da ake yadawa ba gaskiya bane kuma siyasa ce.

    Ya bayyana cewa shugaban kasar bai taba katsalandan a cikin harkokin wata jiha a kasar ba sai dai idan hakan ya shafi tsaron kasar baki daya.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. Za a bai wa sabon sarkin Kano takardar mulki

    A yau Laraba za a bai wa sababbin sarakunan Kano da Bichi takardun tabbatar da su a matsayin sarakuna.

    Sabon Sarkin Kano dai shi ne Alhaji Aminu Ado Bayero, sai kuma sabon Sarkin Bichi shi ne Alhaji Nasiru Ado Bayero.

    An bayyana cewa za a gudanar da taron ba su takardar ne da misalin karfe 3:30 na ranar Laraba.

    .

    Asalin hoton, INSTAGRAM/ADO BAYERO

    Bayanan hoto, AMINU ADO BAYERO
  3. Sabbin 'yan majalisar Kamaru sun yi zamansu na farko

    A Kamaru, zababbun ‘yan Majalisar dokoki 167 da kotun tsarin mulki ta tabbatar da sakamakon zaben da aka yi masu, sun shiga Majalisa a karon farko domin gabatar da kansu a jiya Talata.

    A zaman da su ka yi ne za su tantance juna karkashin wasu kwamitoci 6 da aka kafa, domin gano wanda yake rike da wani mukami da ya saba wa matsayin dan Majalisa.

    Idan aka gano wanda yake cikin wannan hali za a bashi wa’adin kwanaki 10 domin yi wa kanshi zabi, ko ya yi murabus a Majalisa ko kuma a daya aikin.

    Haka ne zai ka iga an bai wa wadannan zababbun wakilai, matsayin cikakkun ‘yan majalisar dokoki.

    Mataki na gaba kuma zai kai ga zaben kakakin majalisa wanda zai fito daga Jam’iyyar da ta fi rinjaye a majalisa.

    Paul Biya

    Asalin hoton, Getty Images

  4. An kara yawan masu gyara Masallacin Ka'aba zuwa 450 da da dare

    Masallacin Ka'aba

    Asalin hoton, Haramain Sharifain

    Masallacin Ka'aba

    Asalin hoton, Haramain Sharifain

    Masallacin Madina

    Asalin hoton, Haramain Sharifain

    Bayanan hoto, Masallacin Madina ma ana ta ci gaba da irin wannan aiki
  5. An tsaurara tsaro a sabon mazaunin Muhammadu Sanusi II

    Sarki Sanusi

    Asalin hoton, Getty Images

    Wakilan BBC da ke garin Awe na jihar Nasarwa da ke arewa ta tsakiyar Najeriya, inda aka ajiye tsohon Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, sun shaida mana cewa jami'an tsaro sun kewaye gidan da yake.

    A halin yanzu, Malam Muhammadu Sanusi na zaune ne a gidan Shugaban Karamar Hukumar Awe.

    Haka kuma, mun samu tabbacin cewa tsohon sarkin yana tare ne da Baffansa, Dan Buran din Kano Munir Sanusi, wanda kuma a lokacin da yake Sarki shi ne shugaban ma'aikatansa.

    Wakilan BBC sun tabbatar da cewa daya daga cikin matansa da daya daga cikin 'ya'yansa mata sun kawo wa tsohon sarkin ziyara a wata mota mai lambar gwamnatin Jihar Kaduna.

    Wasu sarakuna biyu wadanda ba a tantance ko su waye ba sun zo ganin Muhammadu Sanusi amma ba a ba su damar ganinsa ba.

    An hana manema labarai daukar hotuna kuma ba a ba su damar ganinsa ba.

  6. Uganda ta aika wa ofishin jakadancinta $500,000 bisa kuskure

    Ma'aikatar kudin Uganda ta bukaci ofishin jakadancinta a China ya dawo mata da wasu kudi da ta aika bisa kuskure, bayan da aka gano cewa kudin da aka aika an rubanya shi sau goma.

    Majalisar ministocin Uganda ta amince a aika wa dalibai 'yan kasarta da ke birnin Wuhan na China dala 61, 800.

    Amma sai ma'aikatar ilimi ta bukaci dala 600,000.

    A wata sanarwa da ma'aikatar kudin kasar ta fitar ta ce kamata ya yi a aika dala 61, 800 kuma ta ce ta bukaci ofishin jakadancin kasar ya dawo mata da dala 538,200.

    An ta watsa hotunan wasikar ma'aikatar kudin a shgafukan sada zumunta:

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  7. Buhari na da hannu a sauke Muhammadu Sanusi II - Kwankwaso

    Bayanan sautiHira da Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso

    A wata hira da BBC, tsohon gwamnan Kano, Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce "shugabannin gwamnati na Kano su da kansu ne ke cewa umarni aka ba su (su tube Sarki Sanusi). Shi (Buhari) ya ba su umarni".

    Ya yi zargin cewa sabanin maganganun da makusantan Buhari ke cewa, shugaban ba ya tsoma baki cikin irin wadannan rigingimu, "sai dai musamman mu nan a Kano yadda muke gani (Buhari) yana hargitsa inda yake sa hannu".

    "Shugaba Buhari yana tsoma hannu cikin al'amuran jihar Kano", in ji Kwankwaso. "Inda ya kamata ya sa hannun sai mu ga ba nan ya sa hannu ba, inda kuma bai kamata ya sa hannu ba, sai mu ga a nan ya sa hannu".

  8. Manyan mutanen da suka kamu da coronavirus a fadin duniya

    Ministar lafiyar Burtaniya, Nadine Dorries ta kamu da coronavirus kuma ta killace kanta a gida.

    Amma ba ita kadai ce babbar 'yar siyasa a duniya da ta kamu da cutar ba.

    A Faransa, Ministan Al'adu Franck Riester ya kamu da cutar kuma rahotanni sun nuna cewa yana samun sauki.

    Baya ga shi, 'Yan majalisar Faransa biyar suma sun kamu da cutar.

    Nicola Zingaretti

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Nicola Zingaretti

    A Italiya, Shugaban jam'iyyar Democrat Nicola Zingaretti ya kamu da cutar kuma an killace shi a makon jiya.

    Baya ga China, Italiya ce kasar da ta fi ko wacce yawan mutane masu dauke da cutar. Shi ya sa ma aka saka dokar hana shiga da fita a kasar.

    Shugaban Majalisar Taryyar Turai David Sassoli ma ya killace kansa, bayan ya kai ziyara Italiya a karshen makon da ya wuce.

    A Iran ma cutar ta shafi ministoci da 'yan siyasa, inda har 'yan siyasa biyu suka mutu dalilin cutar.

    Fatemeh Rahbar da Mohammad Ali Ramazani da kuma Mohammad Mirmohammadi, wani mai bai wa Ayatollah Ali Khamanei shawara duk sun rasa rayukansu dalilin cutar.

  9. Gwamnatin Kano za ta ci gaba da binciken Muhammadu Sanusi II

    Muhuyi Magaji

    Asalin hoton, INSTAGRAM/KANO ANTI-CORRUPTION

    Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ta jihar Kano a Najeriya ta ce za ta ci gaba da gudanar da bincike kan Sarki Muhammadu Sanusi II bisa zargin badakalar sayar da filaye mallakar masarautar Kano.

    Shugaban hukumar Muhuyi Magaji ya shaida wa BBC cewa cire Sarki Sanusi II daga sarauta zai ba su damar fadada binciken da suke yi a kansa.

    "Ina so mutane su fahimta cewa abin da muke yi a hukumarmu yana da bambanci da abin da ake yi a gwamnati. Wancan [cire Sarki daga kan mulki] abin da gwamnati suke yi mataki ne na mulki. Mu kuma abin da muke yi ya shafi laifuka ne. Saboda haka bincike yana nan, kuma ina ganin wannan wata dama ce da gwamnati ta ba mu ta yin bincike," in ji Muhuyi.

    Bayanan sautiZa a ci gaba da binciken Sarki Sanusi II

    Ku latsa alamar lasifika don sauraren hirar da BBC ta yi da Muhuyi Magaji.

  10. Hotunan yadda rayuwa ke gudana a Italiya bayan saka dokar hana fita

    Kalli hotunan Italiya, kasa mai mutane kusan miliyan 60 da aka sa wa dokar hana fita saboda tsoron yaduwar coronavirus.

    Italy

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Dandalin Duomo a birnin Milan
    Italy

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Wani kare na wucewa ta gaba wani gidan abinci da babu kowa a cikinsa a unguwar Trastevere a birnin Rum
    Italy

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, 'Yan sanda a tsaye a dandalin Duomo a Catania
    Italy

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Wani ma'akacin gidan abinci da babu kwatomomi a Catania
    Italy

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Daidaikun mutane a cikin jirgin kasa
    Italy

    Asalin hoton, Getty

  11. An fara zaman sauraren karar Sowore

    Omoyele Sowore

    A yau ne aka fara zaman sauraren karar mai fafutukar kare hakkin dan Adam din nan dan Najeriya kuma mamallakin jaridar intanet ta Sahara Reporters, Omoyele Sowore a wata babbar kotu da ke Abuja.

    Ana sa rai za a kai 13 ga wannan watan ana zaman.

    A watan Agustan bara ne gwamnatin Najeriya ta kama Mista Sowore bayan da ya sanar da kaddamar da zanga-zangar da ya yi wa taken #RevolutionNow.

    Hukumar tsaro ta farin kaya, DSS ta tsare shi tsawon watanni kafin a sake shi a farkon shekarar nan, bayan zanga-zanga da kiraye-kiraye da kasashen duniya da kungiyoyin kare hakkin dan Adam da suka yi ta yi kan tsare shi.

    Magoya bayan Sowore sun bayyana a gaban kotun da ake shari'ar ta sa, rike da kwalaye kuma suna rera wakokin nuna goyon bayansu gare shi.

    Sowore Trial
    Sowore Trial
    Sowore Trial
  12. Coronavirus: An hana jami'an gwamnatin Ghana fita kasashen waje

    Shugaban Ghana, Nana Akufo Addo ya hana jami'an gwamnati fita kasashen waje na wucin gadi, a yunkurinsa na hana yaduwar cutar coronavirus a Ghana.

    A wata sanarwa da shugabna ma'aikatan kasar, Akusua Frema Osei-Opare ya sa wa hannu, ta ce tafiye-tafiye masu muhimmanci ne kawai za a amince jami'an gwamnatin su yi.

    A yayin bikin cikar kasar shekara 63 da samun 'yancin kai ranar Asabar, Shugaba Akufor Addo ya bai wa 'yan Ghana shawarar daina yin musabiha kuma su rika rufe bakunansu idan suna tari ko atishawa, don han ayaduwar cutar ta COVID-19.

    Kawo yanzu dai cutar ba ta shiga kasar ba.

  13. Mai dauke da HIV ya warke daga cutar

    Mai dauke da cutar HIV

    Asalin hoton, NEW YORK TIMES

    Bayanan hoto, Adam Castillejo

    Likitoci sun tabbatar cewa wani mutumin birnin London ya zama na biyu a duniya da ya warke daga kwayar cuta mai karya garkuwar jiki ko HIV.

    Adam Castillejo har yanzu ba ya dauke da cuta mai karya garkuwar jiki fiye shekara biyu bayan ya daina shan maganin kashe kwayar cutar.

    Sai dai mujallar the Lancet ta ce ba magungunan cutar HIV ne suka warkar da shi ba, illa dashen kwayoyin halitta da aka yi masa saboda cutar daji da yake fama da ita.

  14. Ministar lafiyar Burtaniya ta kamu da coronavirus

    Nadine Dorries

    Ministar lafiyar Burtaniya Nadine Dorries ta kamu da cutar Coronavirus.

    Ministar ta sanar da cewa a yanzu ta killace kanta, yayin da hukumomi ke ta kokarin gano inda takwaso cutar.

    Ko a ranar Alhamis ta halarci wani taron cin abinci da Firanminista Boris Johnson ya shirya a fadar gwamnati da ke titin Downing.

    Wakilin BBC ya ce hukumomi na kokarin gano wadanda ministar ta yi mu'amala da su.

    Kusan mutun 400 ne cutar coronavirus ta kama a Birtaniya inda shida suka mutu.

    Misis Dorries ta ce ta damu matuka kan makomar lafiyar mahaifiyarta mai shekary tamanin da hudu wacce a hanzu haka suke zaune a gida daya.

  15. Barka da safiya

    Barkanku da sake kasancewa da mu a wannan shafi da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da ma sauran kasashen duniya.

  16. Ramphosa ya yi nasara a kotu kan zargin cin hanci

    Cyril Ramaphosa

    Asalin hoton, AFP

    Babbar kotu a Afirka ta Kudu ta yi fatali da binciken da wata kungiyar yaki da cin hanci ta fitar cewa Shugaba Cyril Ramaphosa ya yaudari majalisa kan wasu kudaden tallafin yakin neman zabe.

    A shekarar data gabata wata mai kare jama'a Busisiwe Mkhwebane ta ce ya kamata a binciki Ramaphosa kan tallafin $36,000 da ya karba daga hannun wani kamfani - Bosasa - lokacin yakin neman jagoran Jam'iyya mai mulki ta ANC.

    Ta kuma ce ya kamata a yi bincike a kansa game da almundahana.

    Sai dai kotun ta ce binciken matar sun saba doka sannan bai kamata Mr Ramaphosa ya yi wa majalisa bayanin kudaden kamfe din ba.

    Masu sukar Ms Mkhwebane sun ce dama ta dade tana yi wa kokarin shugaban kasar na yaki da cin hanci makarkashiya.

  17. Hotunan dakin da Muhammadu Sanusi II ya zauna a kauyen Loko

    Loko
    LOKO
    Loko
    LOKO
    Bayanan hoto, Kofar gidan da Muhammadu Sanusi ya zauna a kauyen Loko
    LOKO
  18. Bidiyon yadda ake yi wa sabon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero mubaya'a

    Sabon Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero na nan yana gyara zama a kan karagar mulki, yayin da hakimai da sauran masu sarauta ke ci gaba da yi masa mubaya`a.

    Hankali ya fara kwanciya a birni da kewaye, sabanin jiya da aka yi fama da zaman dar-dar, bayan gwamnatin jihar ta tube Mallam Muhammadu Sanusi na biyu rawani.

    Bayanan bidiyo, Bidiyon yadda ake yi wa sabon Sarkin Kano mubaya'a
  19. An fara rusa Kasuwar Barci ta garin Kaduna

    Kasuwar Barci

    Asalin hoton, Abdullahi Musa Sogiji

    Gwamnatin Jihar Kaduna a arewacin Najeriya ta fara aikin rushe Kasuwar Barci bayan wa'adin da ta bai wa mazauna kasuwar ya cika.

    Tun a wayewar garin Asabar din da ta gabata ne mazauna kasuwar suka tarar da takardar wa'adi like gaban shagunansu inda gwamnatin jihar ta umarce su da su tattara su bar kasuwar.

    Daraktan Hukumar Kula da Raya Birane ta Jihar Kaduna Ismail Dikko ya shaida wa BBC cewa gwamnatin jihar ta Kaduna na da burin sauya fasalin kasuwar ta yadda jama'a daga kasashen ketare za su rinka zuwa kasuwar domin gudanar da kasuwancinsu.

    Ya kuma mayar da martani dangane da korafin da wasu 'yan kasuwar suke yi inda suke cewa an basu wa'adi a kurarren lokaci inda ya bayyana mana cewa doka ta ba su damar bada wa'adi na kwanaki bakwai ko uku.

    'Yan kasuwar barcin sun shaida mana cewa bai kamata a rusa kasuwar ba sakamakon zancen na kotu, sai dai Alhaji Isma'ila Dikko ya shaida mana cewa bai ga wata takarda daga kotu da ta zo ofishinsa ba.

    Kasuwar Barci

    Asalin hoton, Abdullahi Musa Sogiji

    Kasuwar Barci

    Asalin hoton, Abdullahi Musa Sogiji

    Kasuwar Barci

    Asalin hoton, Abdullahi Musa Sogiji

  20. Buhari ya kaddamar da kwamitin ba da shawara na hukumar NDDC

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kaddamar da kwamitin ba da shawara na hukumar bunkasa yankin Neja Delta.

    An yi bikin kaddamar da kwamitin yau Talata a fadar shugaban da ke Abuja babban birnin kasar.

    Gwamnoni da masu ruwa da tsaki daga yankin kudancin kasar sun halarci taron.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X