An gano maganin hana coronavirus yaduwa

Wannan shafin na kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma sauran kasashen duniya har da rahotanni kan coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. An rufe ofishin jakanadancin Norway a Ghana kan coronavirus

    Ghana

    Asalin hoton, Getty Images

    Ofishin jakandancin Norway a Ghana ya tabbatar da cewa daya daga cikin ma`aikatansa ya kamu da kwayar cutar coronavirus (Corvid19).

    Tuni dai aka kebe wanda ya kamu da cutar yayin da aka kulle ofishin jakandancin kafin a bude shi a nan gaba.

    Ofishin kuma ya ce yana zaman tattaunawa da hukumar lafiya ta Ghana domin a bi diddigin wadanda wanda ya kamu da kwayar cutar ya yi cudanya da su.

    An kebe dukkan ma`aikatan ofishin domi dakile yaduwarta.

  2. Ba sai an rage darajar naira ba kan farashin mai – CBN

    Naira

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban Bankin Najeriya CBN ya ce yanayin kasuwa ba ya bukatar a rage darajar Najeriya.

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito babban bankin yana bayyana haka ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

    Darajar naira dai ta fuskanci barazana ne yayin da farashin man fetur ya ragargazo a kasuwar duniya a karshen makon da ya gabata da kuma sabani tsakanin kasar Rasha da Saudiyya kan rage yawan fitar da man.

    Ranar Laraba ne bankin JPMorgan ya bukaci Najeriya ta rage darajar Naira da kashi 10 cikin dari nan da karshen watan Yuni bayan faduwar farashin man fetur.

    Cutar ta kuma shafi yawan yadda ake bukatar man a kasuwar.

  3. Kamfunnan jiragen sama ka iya durkushewa nan da wata 2

    Jiragen sama

    Asalin hoton, Getty Images

    Yayin da tafiye-tafiye tsakanin kasashen duniya ke ci gaba da raguwa saboda annobar coronavirus, wace irin illa hakan zai yi wa kamfunnan jiragen sama?

    • Wata hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta ce kamfunna da dama ka iya durkushewa a cikin wata biyu ko uku
    • Kamfanin British Airways ya ce wasu ma'aikata za su rasa aikinsu - shugaban kamfanin ya ce kamfaninsa yana fama da "wani rikici da ba su taba ganin irinsa ba"
    • Kamfanin Lufthansa na kasar Jamus ya jingine kashi biyu cikin uku na jiragensa, kuma babu mamaki ya nemi taimako daga gwamnatocin kasashen Turai
    • Shi ma Norwegian Air zai iya durkushewa idan bai samu tallafin gwamnati ba - ranar Alhamis ya bayyana cewa zai dakatar da ma'aikata 11,000 sakamakon asarar da ya yi kafin barkewar coronavirus
    • Kamfanin Delta na Amurka ya ce yana tattaunawa da fadar White House domin samun tallafin kudi
  4. Dan sanda mai yi wa Osinbajo rakiya ya mutu a hatsarin mota

    Osinbajo

    Asalin hoton, @ProfOsinbajo

    Bayanan hoto, Osinbajo yana kan hanyarsa ta zuwa filin jirgin saman Abuja hatsarin ya faru

    Ofishin Mataimakin Shugaban Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayar da sanarwar mutuwar daya daga cikin masu yi masa rakiya zuwa filin jirgin Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

    Sufeto Ali Gomina mai shekara 45, ya rasu ne bayan wani hatsari da ya rutsa da shi a bakin aikinsa a yau Juma'a.

    Wata sanarwa da mai taimaka wa Osinbajoi ya fitar, Laolu Akande ya ce mataimakin shugaban kasar ya fasa yin tafiyar sakamakon hatsarin, wanda ya faru a kan titin Nnamdi Azikiwe International Airport.

    "Farfsea Osinbajo ya kadu da mutuwar dan sandan kuma ya bayyana shi a matsayin mai kwazo da hazaka," in ji sanarwar.

  5. Trump ya ki yarda a yi masa gwajin coronavirus

    Shugaba Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ki yarda a yi masa gwajin cutar coronavirus bayan Magajin Garin Miami ya kamu da cutar kwana biyar bayan ya gana da wani jami'in gwamnatin kasar Brazil, wanda kuma ya gana da Trump din a Washington.

    Magajin Gari Francis Suarez yana cikin 'yan siyasar Amurka da suka gana da Shugaban Kasar Brazil Jair Bolsonaro da mukarraban gwamnatinsa - ciki har da mai magana da yawun shugaban da ya kamu da cutar - yayin ziyararsu a South Florida.

    Magajin garin ya umarci wadanda suka yi mu'amala da shi da su dauki matakan kare kansu.

    "Idan ba mu yi musabaha (da ku) ba ko kuma ba mu hadu ba, to in na yi atishawa ba sai kun dauki wani mataki ba," in ji shi.

    Gwaji ya nuna Shugaban Brazil Bolsonaro ba ya dauke da cutar, yayin da Shugaba Trump ya ki yarda a yi masa gwajin.

    Sama da mutum 132,000 ne suka kamu da Covid-19 a kasashen duniya 123 sannan 5,000 suka mutu.

  6. 'Yan sandan Falasdinawa sun hana shiga da fita a Bethlehem

    'Yan sanda a kasar Falasdinu suna aiwatar da dokar ba-sani-ba-sabo a yankin Bethlehem, wanda aka garkame ba shiga ba fita.

    Garin Bethlehem ya kwana biyu a rufe ba shiga ba fita, inda aka rufe otel-otel sannan aka hana masu yawon bude ido shiga duk da cewa garin ya dogara ne kacokam kan yawon bude ido domin samun kudin shiga.

    Falasdinu
    Falasdinu
    Falasdinu
  7. Labarai da dumi-dumi, Nahiyar Turai ce 'cibiyar' coronavirus

    Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ya ce Nahiyar Turai ce "cibiyar" cutar Covid-19, wadda aka fi sani da coronavirus.

  8. El-Rufa'i da Sarki Muhammadu Sanusi II Mai Murabus

    El-Rufa'i da Sarki Muhammadu Sanusi II Mai Murabus

    Asalin hoton, @GovKaduna

    Ga fa gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa’i ya dauko tsohon Sarkin Kano Muhammadu Sanusi daga garin Awe, inda suka durfafi Abuja.

    Ana sa ran tsohon sarkin zai wuce Legas daga Abuja nan gaba.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  9. An dage Champions da Europa League saboda coronavirus

    Zakarun Turai

    Asalin hoton, Getty Images

    Kafatanin wasannin hukumar kwallon kafar Turai ta Uefa da suka hada da Champions League da Europa League, wadanda za a buga a mako mai zuwa, an dage su saboda coronavirus.

    Taron raba kungiyoyi a gasar Europa da za a yi ranar 20 ga watan Maris ma an dage shi.

    A gasar Champions League, wasannin da aka dakatar sun hada da Manchester City v Real Madrid, Juventus v Lyon, Barcelona v Napoli da Bayern Munich v Chelsea.

    A Europa kuma, an dage wasannin Manchester United da na Wolves da Rangers.

    Su ma wasannin matasa na gasar Uefa Youth League da za a yi ranar 17 da 18 ga Maris an dage su.

    Uefa ta ce za ta bayyana ranakun da za a buga wasannin da aka dage din "a lokacin da ya dace".

    Hukumar ta gayyaci wakilai daga kungiyoyi 55 kawayenta zuwa wata ganawa a ranar Talata domin tattauna matakin da za a dauka kan annobar coronavirus.

    Za a tattauna batun dage gasar kasashen Turai ta Euro 2020 a wurin taron.

    Sama da mutum 125,000 ne aka gano suna dauke da cutar coronavirus a kasashe 118 a fadin duniuya, in ji Hukumar Lafiya ta Duniya.

    Wadanda suka mutu kuma sun zarta 4,600.

  10. Hotunan Sarki Aminu Ado Bayero da Gwamna Ganduje a masallacin Juma'a

    Ganduje
    Ganduje
    Ganduje
    Ganduje
  11. Mutum na biyu da ya kamu da coronavirus a Najeriya ya warke

    Ministan lafiya a Najeriya, Osagie Ehanire, ya ce mutum na biyu da ya kamu da cutar coronavirus a Najeriya ya warke.

    Ministan ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a Abuja, inda ya ce daya mai dauke da cutar dan kasar Italiya ya samu sauki kuma za a sallame shi daga asibitin da yake jinya a Legas makon gobe.

    Ministan ya ce Najeriya ba za ta hana jirage ko mutane shiga da fita daga kasar ba, saboda yadda hakan ka iya shafar tattalin arzikin kasar.

    Kwanan nan ne gwamnatin Najeriya ta kafa wani kwamiti don yin bincike tasirin annobar coronavirus ga tattalin arzikin Najeriya.

    Ya kuma ce duka mutanen da suka yi mu'amala da shi sun gama duka gwaje-gwajen da suka dace an kuma tabbatar ba su dauke da cutar, sannan suna iya ci gaba da rayuwarsu yadda suka saba.

    A watan Fabrairu ne Najeriyata samu mutum na farko da ya kamu da coronavirus- wani dan Italiya dan kasuwa da ya zo kasuwanci Najeriya.

    coronavirus

    Asalin hoton, Getty Images

  12. An killace gwamnatin Romania saboda coronavirus

    Shugaban Kasa Klaus Iohannis

    Asalin hoton, Getty Images

    Firai Ministan Riko na kasar Romania, Ludovic Orban da majalisar ministocinsa mai mambobi 17 sun kasance a killace bayan wani sanata dan jam'iyyarsu ta National Liberal Party ya kamu da cutar coronavirus.

    An umarci baki dayan sanatocin jam'iyyar da 'yan jaridar da suka halarci taron manema labaran da gwamnati ta yi da su je a gwada su.

    Tuni dama Romania take cikin rikicin siyasa kuma coronavirus ta kara ta'azzara lamarin.

    Gwamnatin Mista Orban ta yi rashin nasara a kuri'ar yankan kauna da aka kada makonnin da suka gabata, yayin da Shugaban Kasa Klaus Iohannis yake faman neman shugaba domin hade kan kasar da dakile cutar.

    Mutum kusan miliyan 1.2 'yan Romania da ke aiki a Italiya na kokarin komawa gida duk da cewa gwamnati ta roke su da su dakata sannan ta tabbatar cewa mutum 70 sun kamu.

  13. Mutum na farko ya mutu sakamakon coronavirus a India

    India

    Asalin hoton, EPA

    Indiya ta tabbatar da mutuwar mutum na farko da ya mutu sanadiyyar cutar coronavirus, kamar yadda jami'ai suka bayyana.

    Mutumin mai shekara 76 daga jihar Karnataka ya koma kasar ne daga Saudiyya ranar 29 ga watan Fabarairu bayan da ya shafe wata daya a Saudiyyar.

    An fara gano mutanen da suka yi mu'amala da mutumin da ya mutu ranar Talata kuma an kebe su, a cewar ministan lafiya na kasar.

    Mutum 81 ne suka kamu da coronavirus a Indiya, kamar yadda ma'aikatar lafiyar ta sanar.

  14. Buhari ya yi ganawar sirri da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa

    Buhari

    Asalin hoton, @NigeriaGov

    Buhari

    Asalin hoton, @NigeriaGov

    Buhari

    Asalin hoton, @NigeriaGov

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  15. Buhari ya gana da shugaban Guinea-Bissau

    Shugaba Buhari da na Guinea-Bissau,  Umaro Sissoco Embalo

    Asalin hoton, Nigeria Presidency

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin takwaransa na Guinea-Bissau, Umaro Sissoco Embalo.

    Buhari ya tarbi Embalo ne yau Juma'a a fadarsa da ke Abuja, babban birnin kasar.

    Kawo yanzu, babu bayani kan abubuwan da shugabannin suka tattauna a kai.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  16. Muhammadu Sanusi na hudubar Sallar Juma'a a garin Awe

    Tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II na gabatar da hudubar Sallar Juma'a a garin Awe na jihar Nasarawa inda aka kai shi bayan sauke shi daga karagar mulkin sarautar Kano.

    A hudubar da sarkin yake yi, ya yi magana a kan imani da kaddara da kuma hikimomin Ubangiji wajen shirya abubuwa.

    Sarkin ya janyo ayoyi da hadisai da suke nuna muhimmancin yarda da kaddara.

    "Duk abin da Allah Ya kaddara wa mutum to lallai akwai alkhairi a cikinsa,"

  17. Muhammadu Sanusi zai tafi Legas

    Sarki Sanusi

    Asalin hoton, @GOVKADUNA

    Majiya mai karfi ta tabbatar wa da BBC wannan batu, inda ta ce a yanzu tsohon Sarkin zai gabatar da Sallar Juma'a a garin Awe kamar yadda mutanen garin suka bukata.

    Daga na ne kuma shi da gwamnan jihar Kaduna za su tafi Abuja inda daga nan zai kama hanyar zuwa Legas.

    Wannan dai ya biyo bayan umarnin da wata babbar kotu a Abuja ta bayar na cewa a bai wa Muhammadu Sanusi damar shiga ko ina a Najeriya ban da Kano.

  18. Gwamna Ganduje zai je sallar Juma'a a gidan Sarki

    Gwamna Ganduje zai yi sallar Juma'a a gidan Sarki
    Bayanan hoto, Jami'an tsaro na dakon zuwan Gwamna Abdullahi Ganduje a masallacin Juma'a na kofar gidan Sarki

    Bayanai sun nuna cewa Limamin Kano Farfesa Sani Zaharadeen ne zai yi limancin sallar Juma’ar farko da sabon Sarkin Kano Alhajin Aminu Ado Bayero zai halarta, sabanin lokacin da aka nada Muhammadu Sanusi Sarkin Kano, shi ya jagaoranci Sallar Juma’arsa ta farko.

    Amma sai dai Muhammadu Sanusi II ya jagoranci sallar ne a massalacin cikin gidan gwamnatin Kano, a lokacin yana zaune a gidan gwamnati.

    Gwamna Ganduje zai yi sallar Juma'a a gidan Sarki
    Bayanan hoto, Masallacin kofar gidan sarkin ya cika makil da mutane
    Gwamna Ganduje zai yi sallar Juma'a a gidan Sarki
    Bayanan hoto, Masallacin kofar gidan sarkin ya cika makil da mutane
  19. Hotunan Gwamna El-Rufa'i da Muhammadu Sanusi II a garin Awe

    Nasir da Sanusi

    Asalin hoton, @GOVKADUNA/TWITTER

    Nasir da Sanusi

    Asalin hoton, @GOVKADUNA/TWITTER

    Nasir da Sanusi

    Asalin hoton, @GOVKADUNA/TWITTER

  20. Masu coronavirus sun kai 62 a Saudiyya

    Ma'aikatar Lafiya ta Saudiyya ta sanar da cewa an samu karin mutum 17 masu dauke da cutar coronavirus, abin da yasa yawan masu dauke da cutar ya kai 62 a ranar Juma'a.

    A wata sanarwa da ma'aikatar ta fitar ta ce an kuma samu dan kasar na farko da ya kamu da wani mai ita. An killace shi a wani asibiti a Riyadh.Tun a ranar Alhamis majalisar manyan malaman addinin Musulunci ta bayar da wata fatawa, cewa an haramta wa mutanen da suka kamu da cutar Coronavirus halartar sallar Juma'a da sauran sallolin jam'i a masallatai.

    Kamfanin dillancin labaran Saudiyya SPA ya ruwaito cewa an gudanar da taro na 24 na majalisar ce a ranar Laraba don tattauna batun ko ya halatta ko bai halatta ba a halarci sallar Jumma'a da sauran sallolin jam'i a masallatai.

    Majalisar ta kuma yanke shawara cewa, idan har hukumomin da aka dora wa alhakin aiwatar da matakan killace masu alaka da cutar Coronavirus suka bukaci duk wani mutum ya dakata daga halartar sallar Jumma'a da sauran salloli a masallatai, wajibi ne ya bi wannan umarni.