Tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau ya lashe kujerar
sanata a Kano ta tsakiya.
Shekarau na jam’iyyar APC ya samu kuri’u 506,276 inda ya
kada abokin hammayarsa na jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’a 29,775.
A hirarsa da BBC bayan sanar da sakamakon zaben, Shekaru ya ce
babu wani sanata a Najeriya da ya samu yawan kuri’unsa.
Ya kuma yi watsi da zargin cewa ba zai goyi bayan Buhari ba a
majalisar dattawa, yana mai cewa Mahassada ne ke son hada shi da Buhari.
Tsohon gwamnan wanda ya sauya sheka daga PDP zuwa APC dab da zabe ya ce zai ba shugaba Buhari cikakken hadin kai musamman wajen tabbatar da sasanci
tsakanin bangaren majalisa da bangaren
shugaban kasa.