Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Bayanai da rahotanni kan zaben Najeriya na 2019

Wannan shafi na kawo muku yadda jama'a ke bayyana murna kan lashe zaben Najeria da shugaba Muhammadu Buhari ya yi.

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau and Mohammed Abdu

  1. Buhari ya kawo Legas

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kai labari a zaben shugaban kasa a Legas.

    Shugaba Buhari na jam'iyyar APC ya samu kuri'u 580,825 sai kuma Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP ya samu kuri'u 448,015.

  2. Buhari ya yi zarra a Bauchi

    Shugaban Najeria Muhammadu Buhari ya lashe zaben Shugaban kasa a jihar Bauchi inda ya samu kuri'u 798,428 sai kuma Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP ya samu 209, 313.

  3. Sanata Binta Garba bata yi nasara ba a wannan karon

    'Yar majalisar dattawa daya tal daga arewacin Najeriya daga jihar Adamawa ta sha kayen ne a hannun wani dan jam'iyyar PDP. Ita kuma ta yi takarar ne a jam'iyyar APC.

  4. Ra'ayoyi daga shafin Facebook

  5. George Akume bai kai bantensa ba

    Tsohon gwamnan jihar Benue, Sanata George Akume ya sha kaye a kujerarsa ta Sanatan Benue, Arewa maso yamma.

    Dan takarar PDP Orkev Jev ne ya yi nasara.

    Orkev Jev na PDP: 157,776

    George Akume APC: 115,422

  6. Wazirin Adamawa ya yi nasara a Adamawa

    Dan takarar jam'iyyar PDP Atiku Abubakar ya lashe zaben shugaban kasa a jihar Adamawa inda ya samu kuri'u 410,078 sai kuma Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari na APC ya samu 378,078.

  7. Atiku ya samu nasara a Oyo

    Atiku Abubakar dan takarar jam'iyyar PDP ya samu nasarar lashe zaben shugaban kasa a jihar Oyo inda ya samu kuri'u 366,690 sai kuma Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya samu kuri'u 365,229.

  8. Atiku ya doke Buhari a Anambra

    Dan takarar jam'iyyar PDP Atiku Abubakar ya lashe zaben shugaban kasa a jihar Anambra inda ya samu kuri'u 524,738 sai kuma Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya samu 33,298.

  9. Labarai da dumi-dumi, Buhari ya kayar da Atiku a Kaduna

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari na jam'iyyar APC ya yi nasara a jihar Kaduna a zaben shugaban kasa inda ya samu 993,445, yayin da Atiku Abubakar kuma na jam'iyyar PDP ya samu 649,612.

  10. Wane ne zai yi nasara a wadannan jihohi?

  11. Labarai da dumi-dumi, Buhari ya yi nasara a Jigawa

    Hukumar zaben Najeriya ta bayyana shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a matsayin mutumin da ya samu nasarar lashe zaben shugaban kasa a jihar Jigawa inda ya samu kuri'u 794, 738, yayin da abokin hamayyarsa Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP ya samu kuri'u 289, 895.

  12. Buhari ya kayar da Atiku a jihar Naija

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya lashe zaben shugaban kasa a jihar Naija da kuri'u 612,371 sai kuma Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP ya samu 218,052.

  13. Labarai da dumi-dumi, INEC ta dawo daga hutu

    Hukumar zaben Najeriya ta dawo bakin aikin bayyana sakamakon zaben shugaban kasar. A yanzu haka an gayyaci baturiyar zabe da kwamishinan zabe na jihar Naija domin gabatar da sakamakon zaben jihar na shugaban kasa.

  14. Ra'ayoyi kan sakamakon zaben 'yan majalisa

  15. Yadda ake sauraron sakamakon zabe

    Malam Mahmud Abubakar kenan daga jihar Adamawa inda ya kasa ya tsare dab da akwatin rediyonsa yana sauraren yadda hukumar zaben Najeriya, INEC ke karba da bayyana sakamakon zabe.

  16. Ra'ayoyi daga shafin Facebook

  17. Za a ci gaba da bayyana sakamakon zabe da karfe 10:00

    Hukumar zaben Najeriya ta ce ranar Talata za ta ci gaba da bayyana sakamakon zaben shugaban kasa.

    Da daren Litinin ne shugaban hukumar zabe Farfesa Mahmood Yakubu ya sanar da dakatar da tattara sakamakon zaben shugaban kasa zuwa Talata.

    Ya ce za a sake bude cibiyar tattara sakamakon da misalin karfe 10 na safe.

    Yanzu sakamakon jihohi 12 hadi da Abuja babbar birnin Tarayya aka sanar.

    Dan takarar jam’iyyar APC Muhammadu Buhari ya yi nasara ajiha bakwai, yayin da abokin hamayyarsa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya lashe jihohi biyar.

  18. Tanko Almakura da Abdullahi Adamu sun yi nasara a zaben Sanata

    Gwamnan jihar Nasarawa, Umaru Tanko Almakura da tsohon gwamnan jihar Sanata Abdullahi Adamu , dukkansu na jam'iyyar APC sun yi nasara a zaben majalisar dattawan jihar.

    Baturen zaben yankin Farfesa Ahmed Yakubu Ashuku ya ce Tanko Almakura ya samu kuri'a 113,156 yayi da abokin hamayyarsa na PDP, Sulaiman Adokwe ya samu kuri'a 104,595.

    Kazalika Sanaa Abdullahi Adamu ya samu kuri'a 115,298 yayin da abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Bala Ahmed Aliyu, ya samu kuri'a 85,615.

  19. Ndume ya sake cin zaben Sanata daga Borno

    Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar dattawan Najeriya, Sanata Mohammed Ali Ndume, na jam'iyyar APC ya sake yin nasara a zaben majalisar dattawa inda ya samu kuri'a 300, 637 yayin da abokin hamayyarsa na PDP, Kudla Haske, ya samu kuri'a 84, 608, kamar yadda baturen zaben yankin Farfesa Isa Hassan ya bayyana.

    Wannan shi ne karo na uku da Sanata Ndume zai wakilci Kudancin Borno a majalisar dattawan Najeriya.

  20. Abdulaziz Yari ya zama Sanata

    Hukumar zaben Najeriya reshen Zamfara ta ayyana gwamnan jihar Abdulaziz Yari Abubakar a matsayin mutmin da ya yi nasara a zaben kujerar dan majalisar dattawa a mazabar Yammacin Zamfara. Baturen zaben yankin ya ce Gwamna Yari na jam'iyyar APC ya samu kuri'a 153,626 yayin da abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Lawan Hassan, ya samu kuri'a 69,293.