Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Bayanai da rahotanni kan zaben Najeriya na 2019

Wannan shafi na kawo muku yadda jama'a ke bayyana murna kan lashe zaben Najeria da shugaba Muhammadu Buhari ya yi.

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau and Mohammed Abdu

  1. Saraki bai taya dan APC murna kayar da shi ba

    Jami'in da ke kula da watsa labarai na Shugaban majalissar dattijai Sanata Abubakar Bukola Saraki, ya yi watsi da labarin da ake yada wa a kafafen sada zumunta cewar Saraki ya taya dan takarar APC murna kan kayar da shi da ya yi.

    A sanarwar da Yusuph Olaniyonu ya fitar a ranar Litinin ta ce nan gaba Saraki zai yi wa jama'a bayani kan dalillinsa na kin taya abokin hamayyarsa murna.

  2. Rochas Okorocha ya ci zaben Sanata

    Gwamman jihar Imo, Rochas Okorocha na jam'iyyar APC ya lashe zaben kujerar dan majalisar dattawan Yammacin Imo inda ya samu kuri'a 97, 762.

    Gwamna Okorocha ya doke Jones Onyereri na jam'iyyar PDP wanda ya samu kuri'a 63, 117 da kuma Osita Izunaso na jam'iyyar APGA wanda ya samu kuri'a 30, 932.

  3. Jiran sakamakon zaben Nigeria

    Shin nan da yaushe kuke ganin za a sanar da sakamakon zaben Nigeria da aka yi a ranar Asabar.

  4. Surukin Ganduje ya sha kaye a zaben Sanata

    Gwamnan jihar Oyo, Abiola Ajimobi ya fadi zaben dan takarar Sanata a Kudu maso yammacin jihar.

    Mr Ajimobi, wanda shi ne gwamna mai ci na jam'iyar APC ya samu kuri'a 92,218

    Wanda ya lashe zaben shi ne Ademola Balogun na PDP da kuri'a 105,716.

    Gwamna Ajimobi shi ne surukin gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, wanda dansa Idris Ajimobi ya auri Fatima Ganduje.

  5. Ana jiran wakilan hukumar zabe a jihar Cross Rivers

    Wakilan hukumar zabe basu halarci dakin tattara zaben shugaban kasa a jihar Cross Rivers ba.

    Tun a ranar Lahadi jami'an suka sanar cewar za su fara aiki da karfe 9:00 na safe domin tattara sakamakon zaben da aka gudanar a ranar Asabar.

    Sai dai kawo yanzu dan jarida da wani wakilin jam'iyya ne ke wurin.

  6. Mataimakin Saraki ya lashe zaben Sanata

    Mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Ike Ekweremadu, na jam'iyyar PDP ya sake lashe zaben majalisar dattawan Kudancin Enugu.

    Baturen zaben yankin ya ce Ekweremadu ya samu kuri'a 86,088, yayin da abokiyar hamayyarsa ta jam'iyyar APC, Mrs Juliet Ibekaku-Nwagwu ta samu kuri'a 15,187.

    Wannan shi ne karo na biyar da mataimakin shugaban majalisar dattawan ya yi nasara a zaben sanatan yankin.

  7. Karbar sakamakon zaben shugaban kasa a jihar Benue

    Ana ci gaba da karbar sakamakon zaben shugaban kasa a Makurdi, jiha Benue.

    Ya zuwa yanzu an bayyana sakamakon da aka samu daga yankunan kananan hukumomi goma sha uku, saura gona.

  8. Ra'ayoyi daga shafin Twitter

  9. Tattara sakamakon zabe

    An tafi hutun sa'oi biyu a tattara sakamakon zabe a jihar Filato.

    Har yanzu ana jiran sakamakon kananan Hukumomin Jos ta Arewa, da Kanam da Wase da kuma Mangu.

  10. Kabiru Gaya ya sake yin nasara

    Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a majalisar dattawan Najeriya, Kabiru Gaya, ya sake lashe zaben majalisar a karkashin jam'iyyar APC.

    Sanata Gaya ya samu kuri'a 319,004, yayin da abokan hamayarsa na PDP, Abdullahi Rogo ya samu kuri'a 217,520, sannan Yahaya Bala Karaye na jam'iyyar PRP ya samu kuri'a 30,013.

    Baturen zaben yankin Farfesa Ibrahim Barde ne ya bayyana sakamakon zaben.

    Wannan shi ne karo na hudu da Sanata Gaya zai wakilci yankin Kudancin Kano a majalisar dattaan kasar.

  11. Dankwambo ya sha kaye a zaben Sanata

    Gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Hassan Dankwambo na jam'iyyar PDP, ya sha kaye a hannun abokin hamayyarsa na jam'iyyar APC, Sanata Ahmad Alkali, a zaben kujerar majalisar dattawan Arewacin Gombe.

    Baturen zaben yankin, Farfesa Umar Gurama, ya bayyana cewa Sanata Alkali ya samu kuri'a 152,546 yayin da Gwamna Dankwambo ya samu kuri'a 88016.

  12. Buhari ya lashe zabe a karamar hukumar Atiku

    Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP mai hammaya Alhaji Atiku Abubakar ya sha kaye a karamar hukumarsa da ke jihar Adamawa.

    Shugaba Muhammadu Buhari na jam'iyyar APC ne ya samu rinjayen kuri'u a karamar hukumar Yola ta arewa.

    Atiku ya samu kuri'u 27,789, yayin da kuma Buhari ya samu kuri'u 43,865, kamar yadda Dr. Oye babban jami'in da ke tattara sakamakon zaben shugaban kasar na karamar hukumar ya bayyana.

  13. Kai tsaye a shafin Facebook

    Za ku iya garzayawa shafinmu na BBC Hausa Facebook domin kallon labarai da rahotannin da muke kawo muku kan yadda ake bayyana sakamakon zaben Najeriya.

  14. Tsohon gwamnan Abia Orji Uzor Kalu ya lashe zaben sanata

    Tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzor Kalu, ya yi nasara a zaben majalisar dattawa inda zai wakilci Arewacin jihar a majalisar dattawan kasar.

    Kalu, wanda ya tsaya takara a karkashin jam'iyyar APC ya samu kuri'a 30,580 inda ya doke Mao Ohuabunwa na jam'iyyar PDP, wanda ya samu kuri'a 21,940.

  15. Labarai da dumi-dumi, Dukkan sanatocin Ekiti sun sha kaye

    Dukkan sanatoci uku na jam'iyyar PDP da ke wakiltar jihar Ekiti a majalisar dattawan Najeriya sun sha kaye a zaben 'yan majalisar dattawan kasar.

    Sanata Biodun Olujimi da Sanata Duro Faseyi da kuma Sanata Obafemi Adewale duk basu yi nasara a zaben ba.

    Abokan hamayyarsu na jam'iyyar APC ne suka yi nasara a zaben.

    Sabbin sanatocin da aka zaba su ne; Opeyemi Bamidele, Prince Adedayo Adeyeye da kuma Olubunmi Adetumbi.

  16. Yakubu Dogara ya lashe kujerarsa a Bauchi

    Kakakin majalisar wakilan Najeriya Yakubu Dogara ya lashe kujerarsa ta dan majalisar tarayya a jihar Bauchi.

    Hukumar zabe ce ta tabbatar da Dogara a matsayin wanda ya lashe zaben dan majalisar tarayya da ke wakilatar Balewa da Bogoro.

    Dogara na jam'iyyar PDP ya samu kuri'u 73,609, inda ya doke babban abokin hamayyarsa Dalhatu Kantana na APC wanda ya samu kuri'u 50,078.

    Hakan dai na nufin Dogara wanda ya sauya sheka daga APC zuwa PDP kafin zabe zai sake dawo wa majalisar tarayya, kuma akwai alamun zai nemi kare kujerarsa ta kakakin majalisar wakilai.

  17. Bukola Saraki ya sha kaye a zaben majalisar dattawa

    Shugaban Majalisar dattawa Bukola Saraki ya sha kaye a Kwara ta tsakiya da yake wakilta a majalisa.

    Sakamakon wanda hukumar zabe ta sanar an tabbatar da Saraki ya fadi a dukkanin kananan hukumomi hudu da yake wakilta.

    Dan takarar APC ne Ibrahim Oloriegbe ya kayar da Saraki a yankin Kwara ta tsakiya da ya kunshi kananan hukumomin Ilori ta yamma da Ilori ta Kudu da Ilori ta gabas da kuma Asa.

  18. Dino Melaye ya yi nasara a zaben sanatan Kogi

    Hukumar zaben Najeriya reshen jihar Kogi ta ayyana Sanata Dino Melaye a matsayin mutumin da ya lashe zaben majalisar dattawan Yamma.

    Baturen zaben jihar, Farfesa Emmanuel Bala, ya bayyana cewa Sanata Melaye na jam'iyyar PDP ne ya lashe zaben da kuri'a 85,395

    Sanata Melaye ya doke abokin hamayyarsa na jam'iyyar APC, Smart Adeyemi wanda ya samu kuri'a 76,902.

  19. Barkan mu da warhaka

    Nasidi Adamu Yahaya ne yake yi muku barka da warhaka. Da fatan za ku bibiye mu domin samun bayanai da rahotanni kai tsaye kan yadda ake bayyana sakamakon zaben Najeriya da aka gudanar ranar Asabar. Ku leka shafinmu na BBC Hausa Facebook domin tafka muhawara da bayyana ra'ayoyinku.

  20. Sai gobe

    A nan muka kawo karshen bayanai da rahotanni da muke kawo ma ku kai tsaye kan zaben Najeriya da aka gudanar ranar Asabar inda ake jiran sakamakon zaben. Ku tara gobe inda za mu ci gaba da kawo maku bayanai har zuwa lokacin bayyana sakamakon. Mustapha Musa Kaita da Awwal Ahmad Janyau ke ma ku fatan alkhairi.