Afcon 2021: Hotunan yadda Super Eagles ta casa Sudan

An wallafa

Najeriya ta barje gumi da Sudan a yau Asabar a wasan rukunin na biyu a gasar cin kofin Afirka da ake gudanarwa a Kamaru.

An yi wasan ne a Garoua filin wasa na Roumde Adjia inda rukuni na hudu da ya kunshi Najeriya da Masar da Sudan da kuma Guinea Bissau suke ta su fafatawar.

G

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Cikin minti na uku da fara wasan dan wasan gaban Najeriya Samuel Chukwueze ya jefa kwallon farko a wannan wasa
G

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Ndidi da Simon lokacin da ake murnar cin kwallo ta biyu a dokewar da Spuer Eagles ta yi wa Sudan
G

Asalin hoton, DANIEL BELOUMOU OLOMO

Bayanan hoto, Wasan ya bai wa Najeriya damar tsallakawa zagaye na yan 16 na gasar
g

Asalin hoton, DANIEL BELOUMOU OLOMO

Bayanan hoto, Bayan Najeriya ta jefa kwallo ta uku ta samu nutsuwa a wasan duk kuwa da cewa daga baya ta fuskanci matsi daga hannun Sudan
G

Asalin hoton, DANIEL BELOUMOU OLOMO

Bayanan hoto, Matsin da Sudan ta yi ya sanya ta samu damar zare kwallo guda ta hannun dan wasanta Daiyeen ta hanyar bugun daga kai sai mai tsaron gida
G

Asalin hoton, DANIEL BELOUMOU OLOMO

Bayanan hoto, Tun bayan kwallo ta uku da Najeriya ta ci ba ta samu damarmaki ba kamar yadda ta samu a minti 45 din farko