Afcon 2021: Hotunan yadda Super Eagles ta casa Sudan

An wallafa

Najeriya ta barje gumi da Sudan a yau Asabar a wasan rukunin na biyu a gasar cin kofin Afirka da ake gudanarwa a Kamaru.

An yi wasan ne a Garoua filin wasa na Roumde Adjia inda rukuni na hudu da ya kunshi Najeriya da Masar da Sudan da kuma Guinea Bissau suke ta su fafatawar.