Amurka: Trump ya ci gaba da yaƙin neman zaɓe

Mai ɗkin shugaba Trump Melania Trump yayin da take gabatar da shi

Asalin hoton, Reuters

An wallafa

Shugaba Trump ya yi yaƙin neman zaɓe na farko a jihar Georgia tun bayan faɗuwa zaɓe, a wani mataki na mara baya ga ƴan takarar maajalisar dattawan ƙasar daga jihar Georgia da za a gudanar da zagaye na biyu na zaɓensu a watan Janairu.

Shugaban ya faɗa wa dandazon mutanen da suka taru a Valdosta cewa shi ne ya lashe zaɓen jihar da aka gudanar, duk da cewa ba shi aka sanar a hukumace ba.

Duk da ya yi zargin an tafka maguɗi a zaɓen, ya bukaci magoya bayansa su fita su jefa ƙuri'unsu, sannan kar cuwacuwar da yake cewa an yi ta rage musu ƙwarin gwiwar samun nasara a zaben.

Ya ce Amurka za ta faɗa hannun ƴan gurguzu matsawar jam'iyyar Democrat ta lashe kujeru biyu na ƴan majalisar da za a kara a kansu.

Wasu magoya bayan jam'iyyar Republican na fargabar cewa ci gaba da zargin tafka maguɗi a zaɓen da Mista Trump ke ta faman yi har zuwa yanzu na iya sa wa su kasa samun nasara a zaben da yake da matuƙar muhimmanci.

Fargabar ita ce, masu zaɓe na iya fitar da rai da cewa za a yi adalci a zaɓen, sakamakon kalaman da shugaban na Amurka ke ci gaba da furtawa.

Tun farko, shugaban ya yi ƙoƙrin ganin gwamnonin jihohin da yake zargin an yi maguɗi a cikinsu waɗanda na Republican ne sun taimaka masa domin yin watsi da sakamakon zaben na ranar 3 ga watan Nuwamba.

Republcan ce ke jagoranci a wasu jihohi a zaben majalisar dokoki, ana gudanar da bincike na musamman kan zargin maguɗi a zaben da kwamitin yaƙin neman zaben shugaba Trump ke yi.

Kotuna da dama a sassan kasar daban-daban sun yi watsi da iƙirarin cewa an samu kura-kurai, ko ma wata ƙulla-ƙulla da sunan taimaka wa jam'iyyar Democrat ta su Zababben Shugaba Joe Biden.