Ƴan sanda sun gurfanar da ƙarin mutum 17 bisa zarginsu da hannu a kisan maraban Jos

Asalin hoton, Getty Images
Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta sanar da gurfanar da wasu ƙarin mutane 17 da ake zargi da hannu a kisan gayyan da aka yi wa wata mata a Ungwar maraban Jos, na jihar Kaduna a makon da ya gabata.
Wata sanarwar da ta fito daga ofishin jami'in hulɗa da jama'a na rundunar DSP Mansir Hassan ta ce an gurfanar da waɗanda ake zargin ne yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.
Sabarwar ta ƙara da cewa bayan kammala binciken farko, an gurfanar da wasu mutane talatin da uku (33) da ake zargi da laifin haɗa baki da kuma yin taro ba bisa ƙa’ida ba.
Rundunar ta kuma bayyana cewa mutane talatin (30) da aka kama bayan aukuwar lamarin, ba same su da hannu wajen aikata laifin ba, kuma an sake su ba tare da wani sharaɗi ba.
Rundunar ta sake nanata cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, inda ta bayar da tabbacin cewa ta na ƙara ƙaimi wajen ganowa da kamo duk waɗanda ke da hannu, ko kuma suka taimaka wajen aikata wannan laifi.






























