An kusa bude Masallatan Haramin Makkah da Madina - Sudais

Asalin hoton, @HaramainInfo
Shugaban Masallatan Harami guda biyu masu daraja a Saudiyya Shaikh Abdurrahman Sudais, ya ce lokaci ya kusan zuwa da za a dawo yin ibadah a masallatan biyu da ke Makkah da Madina.
Hakan ya bayyana ne a wata sanarwa da shafin Masallatan na Facebook Haramain Sharifain ya wallafa a ranar Talata.
Wani bidiyo ke yawo a kafofin sadarwa na intanet. Sheikh Al-Sudais ya ce: "lokaci na zuwa da fargaba za ta gushe daga al'ummar musulmi kuma za mu dawo masallacin harami domin dawafi da safa da marwa da kuma yin ibadah a masallacin Annabi SAW."
"Abubuwa za su dawo, da izinin Allah kamar yadda suke," in ji Sudais.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
Jaridar Saudi Gazette ta ruwaito ma'aikatar kula da ayyukan Hajji da Umrah na cewa "da yardar Allah karkashin jagorancin gwamnatinmu, da kuma kiyaye umurnin hukumomi, abubuwa za su dawo daidai a Makkah da kuma kai ziyara Masallacin Annabi a Madina daga Musulmi a sassan duniya.
Tun da farko, Sheikh Al-Sudais ya jagoranci dasa kamarori a Masallacin Harami da za su gano wanda ke dauke da cutar korona.
Kamarorin za su iya gano yanayin zafin jikin mutane kusan 25 a lokaci guda, an dasa su a kofar shiga Masallatan Harami a Makkah da Madina.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 3
Duk wannan karfafa guiwar, amma babu tabbas ko za a gudanar da gudanar da Aikin Hajji a bana, yayin da gwamnatin Saudiyya ta nemi kasashen duniya su dakatar da karbar kudaden jama'a domin zuwa aikin Hajji, a yayin da annobar coronavirus ke ci gaba da mamaye duniya.
Tuni hukumomin Saudiyya suka hana shiga Makkah da Madina, da ma Riyadh babban birnin kasar, a kokarin da hukumomin kasar ke yi na hana yaduwar Covid-19.
Hukumomin lafiya a Saudiyya sun ce zuwa yanzu mutum 1,325 suka kamu da cutar korona a kasar, kuma kashi 85 daga cikinsu 'yan kasashen waje ne.










