An samu karin mutum biyar masu coronavirus a Najeriya

Asalin hoton, Getty Images
An samu karin mutum biyar masu coronavirus a Najeriya in ji hukumar da ke kare yaduwar cututtuka ta kasar.
Hukumar yaki da yaduwar cutuka a Najeriya ce ta tabbatar da hakan a ranar Laraba a shafinta na Twitter.
Hukumar ta ce duka masu dauke da cutar sun dawo ne daga Burtaniya ko Amurka kwanan nan.
A cewarta, a cikin mutanen har da wata mata da jaririyarta mai mako shida a duniya da kuma wani dan Amurka, wanda ya shiga kasar ta tsandauri, inda ya kasance mutum na farko da ya shigo da cutar ba ta jirgin sama ba.
Hukumar ta ce an tattara bayanai kan dukkan mutanen da zummar gano wadanda suka yi mu'amala da su.
Ta yi kira ga 'yan Najeriya da su kwantar da hankalinsu yayin da jami'an kiwon lafiya ke daukar dukkan matakan da suka dace don yaki da yaduwar cutar a kasar.
Kawo yanzu mutum takwas ne aka tabbatar suna dauke da cutar a Najeriya.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X








