Yadda Anthony Joshua ya yi gaisuwar ban girma ga Buhari

Anthony Joshua prostrating before Muhammadu Buhari

Asalin hoton, Tolu Ogunlesi

Bayanan hoto, Anthony Joshua ya yi gaisuwar ban girma ga Shugaba Muhammadu Buhari
An wallafa

Wasu hotuna da suka watsu a kafafen sada zumunta sun nuna fitaccen dan wasan damben nan dan Birtaniya Anthony Joshua zube a kasa da ke nuna alamar gaisuwar ban girma irin ta kabilar Yarabawa ga Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari a birnin London.

Joshua, wanda asalinsa dan Najeriya ne, ya fada wa jama'a cewa zai tsaya tsayin-daka wajen kare Najeriya a duk lokacin da aka bukaci hakan.

Mutane da dama sun bayyana mabambantan ra'ayoyi game da hotunan inda masu sukar Shugaba Buhari ke nuna takaici kan yadda dan damben ya ki bayyana irin dimbin kalubalen da matasan Najeriya ke fuskanta.

Sai dai tuni Joshua ya mayar da martani ta shafinsa na Instagram inda yace "wannan ba batu ne na siyasa ba. Batu ne na al'ada da kuma girmama na gaba da mu."

Wasu kuwa yaba wa Joshua suka yi kan yadda ya rungumi tsatsonsa Najeriya da kuma yadda ya nuna girmamawa ga Shugaba Buhari ta hanyar yin gaisuwar da aka san kabilar Yarabawa da yi.

Anthony Joshua taking a selfie with Muhammadu Buhari

Asalin hoton, Tolu Ogunlesi

Bayanan hoto, Hoton Buhari da Joshua a London

Shugaba Buhari na birnin London domin halartar taron zuba jari na Birtaniya da Afirka na farko wanda aka fara ranar 20 ga watan Janairu.

Daya daga cikin masu taimaka wa Shugaba Buhari, Tolu Ogunlesi, ya wallafa wasu hotunan taron a shafinsa na Twitter inda ya ce: "AJ! Shi da shugaban kasa a yau."