Afcon 2023: Salah ba zai buga wa Masar wasa biyu ba

Asalin hoton, Getty Images
Mohamed Salah ba zai buga wa Masar karawar da za ta yi da Cape Verde ba ranar Litinin a gasar cin kofin nahiyar Afirka, sakamakon raunin da ya ji.
Haka kuma dan kwallon Liverpool ba zai yi wa Masar wasa daya a zagaye na biyu ba, koda Masar za ta kai zagayen kungiyoyin 16.
Salah ya ji rauni a wasan da Masar da Ghana suka tashi 2-2 ranar Alhamis a karawar cikin rukuni na biyu.
Kenan Salah zai kara buga wa Masar wasa ne idan tawagar ta kai zagayen daf da na kusa da na karshe da za a yi ranar biyu da uku ga watan Fabrairu.
Tun a ranar Juma'a kociyan Liverpool, Jurgen Klopp ya ce Salah na tare da gajiya, wanda wasa 10 ne bai buga ba a lik a kaka shida a Liverpool.
Rashin Salah a tawagar Masar zai sa tawagar ta fuskanci kalubale a Afcon, bayan da ta fara wasannin da ake yi a Ivory Coast da kasa taka rawar da ta dace.
Salah ne ya ci Mozambique ranar Lahadi da suka tashi 2-2 a wasan farko a gasar kofin Afrka, sannan ta tashi 2-2 da Ghana.
Masar mai maki biyu a rukuni na biyu na bukatar cin Cape Verde mai maki shida, idan har tana son buga zagaye na biyu a babbar gasar tamaula ta Afirka.
Rabon da Masar ta dauki gasar kofin Afirka tun 2010, ita ce kan gaba a yawan lashe kofin mai bakwai jimilla.











