Tawagar ƙwallon Australia za ta bai wa Falasɗinawa gudummawa

Australia

Asalin hoton, BBC Sport

An wallafa

Australia za ta bayar da wani ɓangare na kuɗin wasan da za ta yi da Falasɗinawa a gurbin neman shiga gasar cin kofin duniya don ayyukan jin kai a Gaza.

Hukumar ƙawallon ƙafa ta Australia ta ce za ta ba da kwatankwacin abin da tawagar Socceroos ɗin za ta bayar.

Kocin Australia Graham Arnold ya ce shirye-shiryen wasan na ranar Talata ya kasance "mai matukar damuwa" dangane da rikicin Isra'ila da Gaza.

An shirya gudanar da wasan ne a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan amma jami'ai sun sauya wurin zuwa Kuwait.

Sama da mutane 1,200 ne aka kashe a jerin hare-haren da ƙungiyar Hamas ta ƙaddamar a Isra'ila tare da yin garkuwa da mutane kusan 240, yayin da hukumomin kiwon lafiya na Gaza suka ce an kashe fiye da 11,000 a yankin.

Falasɗinawa sun buga wasansu na farko tun farkon rikicin ranar Alhamis, inda suka tashi canjaras 0-0 da Lebanon a Sharjah.