FA Cup: Man City ta kai quarter finals bayan cin Bristol City

Manchester City

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa

Manchester City ta je ta ci Bristol City 3-0 a wasan zagaye na biyar a FA Cup ranar Talata ta kuma kai daf da na kusa da na karshe.

Phil Foden ne ya ci biyu da kuma Kevin De Bruyne ya zura na uku a ragar kungiyar da ke buga Championship a fafatawr da suka yi a Ashton Gate.

Kungiyar da Pep Guardiola ke jan ragama ta ci wasa 11 a waje a jere a FA Cup, wadda ke fatan daukar na bana kuma na bakwai jimilla.

Za a ci gaba da wasannin zagaye na biyar ranar Laraba:

  • Southampton da Grimsby Town
  • Burnley da Fleetwood Town
  • Manchester United da West Ham United
  • Sheffield United da Tottenham
Fa Cup

Asalin hoton, BBC Sport