Najeriya ta ci Kamaru ta samu gurbin gasar kofin duniya

Nigeria vs Cameroon

Asalin hoton, Caf twitter

An wallafa

Tawagar kwallon kafa ta mata ta Najeriya ta doke ta Kamaru da ci 1-0 a wasan daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin Afirka da suka kara ranar Alhamis.

Minti 11 da komawa zagaye na biyu Falcons ta ci kwallo ta hannun Rasheedat Ajibade a wasan na hamayya da suka kara a Casablanca.

Da wannan sakamakon Super Falcons ta samu kai wa zagayen daf da na karshe ta kuma samu gurbin shiga gasar kofin duniya da za ta wakilci Afirka a badi.

Wannan shi ne karo na 12 da Supeer Falcons ta kai daf da karshe a gasar kwallon kafa ta mata ta cin kofin Afirka.

Haka kuma karo na tara a jere da Falcons za ta wakilci Afirka a gasar cin kofin duniya da za a yi a 2023.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

Karshen labarin da aka sa a X

Tun farko an tsara cewar duk kasahe hudun da suka kai daf da karshe a wasannin bana, za su wakilci Afirka a gasar cin kofin duniya da za a yi a New Zealand da Australia.

Koda yake an yi waje da Indomitable Lionesses daga gasar kofin Afirka, sai dai tana da damar samun gurbin kofin duniya a badi da za a tantance ranar Lahadi.

Bayan da Afirka ta Kudu ta doke Najeriya a wasan farko, daga nan Falcons ta kara sa kaimi, inda ta doke Burundi da kuma Botswana.

Falcons za ta buga karawar daf da karshe da mai masaukin baki Morocco.