Najeriya ta ci Kamaru ta samu gurbin gasar kofin duniya

Asalin hoton, Caf twitter
Tawagar kwallon kafa ta mata ta Najeriya ta doke ta Kamaru da ci 1-0 a wasan daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin Afirka da suka kara ranar Alhamis.
Minti 11 da komawa zagaye na biyu Falcons ta ci kwallo ta hannun Rasheedat Ajibade a wasan na hamayya da suka kara a Casablanca.
Da wannan sakamakon Super Falcons ta samu kai wa zagayen daf da na karshe ta kuma samu gurbin shiga gasar kofin duniya da za ta wakilci Afirka a badi.
Wannan shi ne karo na 12 da Supeer Falcons ta kai daf da karshe a gasar kwallon kafa ta mata ta cin kofin Afirka.
Haka kuma karo na tara a jere da Falcons za ta wakilci Afirka a gasar cin kofin duniya da za a yi a 2023.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Tun farko an tsara cewar duk kasahe hudun da suka kai daf da karshe a wasannin bana, za su wakilci Afirka a gasar cin kofin duniya da za a yi a New Zealand da Australia.
Koda yake an yi waje da Indomitable Lionesses daga gasar kofin Afirka, sai dai tana da damar samun gurbin kofin duniya a badi da za a tantance ranar Lahadi.
Bayan da Afirka ta Kudu ta doke Najeriya a wasan farko, daga nan Falcons ta kara sa kaimi, inda ta doke Burundi da kuma Botswana.
Falcons za ta buga karawar daf da karshe da mai masaukin baki Morocco.









