NPFL: Enyimba ta kori kocinta Usman Abdallah

Asalin hoton, @EnyimbaFC
Kungiyar Enyimba mai rike da kofin gasar Firmiyar Najeriya ta Nigerian Professional Football League (NPFL), ta kori kocinta Usman Abdallah a ranar Litinin.
Wani bayani da kungiyar ta fitar a yau Litinin ya bayyana cewa korar ta fara aiki ne nan take, sannan ta ce Fatai Osho ne zai maye gurbinsa na rikon kwarya.
Korar Abdallah ta zo ne bayan kashin da kungiyar ta sha 0-4 a hannun Plateau United ranar Lahadi.
Enyimba tana matsayi na 13 a teburin Firimiyar bayan wasa 10, inda ta ci hudu kacal.
"Bayan fuskantar sakamako marasa dadi, kungiyar ta amince cewa wajibi ne ta sauya salon wasanta a gida da kuma nahiyar Afirka," Enyimba ta bayyana.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Shugaban kungiyar Felix Anyansi Agwu ya ce: "Wannan mataki ba abu ne da muka dauka cikin sauki ba ko kuma hanzari".






