Premier League: Arsenal ta sake barar da damarta

Asalin hoton, Getty Images
An wallafa
Wani sabon makon ya wuce ya bar Arsenal da barar da nasarar da ta yi a kan Wolves a filin wasa na Emirate.
Pierre-Emerick Aubameyang ne ya bai wa Arsenal nasara tun a minti na 21 bayan an bar shi ba tare da wani tsaro ba, inda ya ci kwallonsa ta 50 ga Arsenal.
Sai a minti na 76 ne Raul Jimenez ya farke wa Wolves tare da taimakon Joao Moutinho.
Wannan dai kusan maimaici ne na abin da ya faru a makon da ya gabata, inda Arsenal din ta kasa cin wasa bayan ta zira kwallo biyu a ragar Crystal Palace.
Wolves tana mataki na 11 daga maki guda dayan da ta samu, yayin da Arsenal take a mataki na biyar.







