Andres Iniesta zai bar Barcelona a karshen kakar bana

Asalin hoton, EPA
Kaftin din Barcelona, Andres Iniesta, ya ce zai bar kungiyar da ke kasar Spain a karshen wannan kakar.
Dan wasan na tsakiya, mai shekara 33, ya buga wasanni 669, inda ya ci kofi 31 a Barcelona.
Iniesta kuma ya ci wa Spain kofin duniya da kofin Turai guda biyu.
Ya kasance muhimmin dan wasa a Barcelona, inda a nan ne ya fara taka leda tun kuriciyarsa.
A lokacin da yake bayar da sanarwar cewa zai bar kungiyar, Iniesta ya ce "wannan wata rana ce mai wahala a gare ni"
Iniesta, ya buga wa Spain wasanni 125, kuma yana cikin 'yan wasan kasar da za su buga gasar cin kofin duniya a Rasha a bana.
Ya ci gasar cin kofin duniya a shekarar 2010 da gasar cin kofin kasashen Turai a 2008 da kuma 2012 - baya ga gasar zakarun Turai hudu da kuma gasar La Liga takwas da ya lashe - tare da wasu kofuna da dama da ya ci wa Barcelona.







