Tanzania za ta rufe makarantu saboda coronavirus
Hukumomi a Tanzania sun sanar da cewa za su rufe dukkan makarantun kasar a wani mataki na hana yaduwar cutar coronavirus.
Za a rufe makarantun ne ranar Laraba tsawon kwana 30, a cewar Firai Minista Kassim Majaliwa.
Ya kara da cewa an dakatar da dukkan tarukan jama'a, ciki har da wasannin kwallo.
An dauki matakin ne bayan an gano cewa wani dan kasar mai shekara 46, wanda ya koma Tanzania daga Belgium, yana dauke da cutar Covid-19.
An gano mutane da dama da suka yi mu'amala da shi kuma an killace su, in ji Mr Majaliwa.
A cewarsa, ana neman sauran mutanen da suka yi mu'amala da mutumin.
Mr Majaliwa. ya ce a shirye Tanzania take ta tunkari Covid-19 idan ta ci gaba da yaduwa a kasar.

Asalin hoton, Getty Images















