Gwamnatin Kamaru ta dauki wasu matakai 13 da za su fara aiki daga yau 18 ga
watan Maris kan coronavirus
An dauki matakan bayan wani taron gaggawa da Firaminista
Joseph Dion Ngute ya shugabanta, wanda kuma daukacin majalisar Gwamnati ta
halarta.
Sakamakon wannan taron ya bayyana cewa za
a rufe duka iyakokin kasar ta sama da ta ruwa da ta kasa. Sa’annan kuma za a
daina ba da takardun izinin shiga Kamaru daga kasashen ketare.
Za a rufe ajujuwa a makarantun boko ta kasa, na
Gwamnati da masu zaman kansu daga firamare har izuwa jami’a tare da dakatar da yin karatu.
Hakanan kuma an hana shirya duk wasu
taruka da suka kunshi mutane sama da 50.
Duka gidajen cin abinci da mashaya
hadi da wasu wuraren nishadi za su kasance a rufe.
Ya kamata kuma mutane su takaita yin
zirga-zirgar da suke yi, wato su kiyayi yin balaguro ba tare da wasu kwararan
hujjoji ba.
Su kuma direbobin motocin haya na bas da na tasi za su daina cunkusa mutane a cikin ababan
hawansu.
Ma’aikatun Gwamnati kuma za su fi maida
hankali wurin yin musayar sakwanni a tsakaninsu ta hanyar intanet.
Sai dai kuma za a bar jiragen daukar kayan abinci da wasu kayan kasuwanci suna zirga-zirga.
Hakanan ma duk wasu 'yan Kamaru da suke
ketare, har idan akwai wata bukatar da suke dauke da ita a cikin kasa, na iya
tuntubar ofishin jakadancin Kamaru a kasar da ta karbi bakwancinsu domin samun
izinin shiga kasa.