Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da suka faru a Najeriya da wasu sassan duniya

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma wasu sassan duniya, musamman rahotanni kan annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Buhari Muhammad Fagge

  1. Budewa

    Rahotannin ranar Alhamis 18 ga watan Maris 2020

    Masu bin mu a wannan shafi assalamu alaikum. Halima Umar Saleh ce take muku fatan kun wayi gari lafiya.

    Yau ma kamar kullum za mu dora daga inda muka tsaya jiya wajen kawo muku labarai da rahotannin abubuwan da ke faruwa a duniya kan annobar coronavirus.

    Amma za mu dinga tavbo wasu batutuwan daban bayan coronavirus din.

    Kuna iya komawa kasan wannan shafi don karanta abubuwan da suka faru a jiya Laraba idan har ba ku samu karanta su ba.

  2. Sai da safenku

    Karshen rahotannin kai-tsaye ke nan.

    Muna sa ran za ku duba kasa domin karanta su da kuma komawa babban shafinmu domin kallon hotuna da bidiyo.

    Umar Mikail ke cewa mu zama lafiya.

  3. Coronavirus: N125 ne sabon farashin man fetur a Najeriya

    Daga ranar Alhamis 19 ga watan Maris (gobe) za a fara sayar da man fetur kan naira 125 a kan lita daya a gidajen man NNPC a kasa baki daya.

    Shugaban kamfanin man Najeriya na NNPC, Mele Kyari ne ya bayyana haka a wata sanaarwa da ya fitar, wanda ya ce ragin ya biyo bayan umarnin da karamin ministan man fetur ya bayar ne.

    A wata sanarwa da karamin ministan man fetur Timipre Sylva ya fitar ranar Laraba, ya ce gwamnati ta rage farashin ne domin 'yan Najeriya su amfana da faduwar farashin danyen man a kasuwar duniya.

    Farashin mai ya ragargazo daga dala $60 a 'yan makonnin nan sakamakon kamarin da cutar coronavirus take ci gaba da yi a duniya, inda yanzu man yake reto tsakanin dala $29 zuwa $30.

  4. Birtaniya za ta samar da kayan gwajin coronavirus daga gida

    Gwamnatin Birtaniya ta ce tana aiki domin samar da kayan gwajin cutar coronavirus a gida ba sai an je asibiti ba.

    Dr Jenny Harries, mataimakiyar sakataren lafiya ce ta bayyana hakan a wani taron manema labarai da suka gudanar tare da Firai Minsita Boris Jhonson.

    Ta ce yanzu gwamnati ta kara yawan gwajin cutar zuwa 25,000 a duk rana.

    "Yayin da muke ci gaba (da yaki da coronavirus), muna da buri sosai na samar da gwaje-gwaje a gida saboda ba ma son masu dauke da cutar su rika zuwa asibiti," in ji ta.

  5. Labarai da dumi-dumi, Coronavirus: Mutum 475 sun mutu a Italiya a rana guda

    Wadanda suka mutu a Italiya sakamakon coronavirus sun karu da mutum 475 a cikin awa 24 da suka gabata, in ji mahukunta.

    Hakan ya sa wadanda suka mutu jumulla ya zama mutum 2,978 a kasar - an samu karuwar kashi 19 cikin 100 ke nan.

    Mutunen da suka kamu a kasar, wadda cutar ta fi addaba a Nahiyar Turai, sun karu daga 31,506 zuwa 35,713.

  6. Coronavirus: Fiye da mutum dubu 200 ne suka kamu a duniya

    Yanzun nan Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta gama gudanar wani taron manema labarai.

    Ga abin da muka tsakuro muku daga ciki:

    • Fiye da mutum 200,000 ne suka kamu da coronavirus a fadin duniya.
    • Fiye da mutum 8,000 ne suka mutu.
    • Akasarin wadanda suka kamu - kashi 80 cikin 100 - a Nahiyar Turai suke da kuma yankin Western Pacific, wanda ya hada da bangare mai yawa na Nahiyar Asiya.
    • Nesanta kai daga jama'a, kamar soke taruka, ka iya taimakawa wurin rage yaduwar cutar.
    • "Amma idan ana son kawo karshen annoba, wajibi ne kasashe su killace, su yi gwaji, su bayar da kulawa sannan su bibiyi masu dauke da ita," in ji shugabn WHO.
    • Hukumar WHO da abokan huldarta suna gudanar da wani bincike na hadin gwiwa
    • Sannan ta bukaci mutane a Afirka da su guji taruwar jama'a.
  7. Buhari ya rage farshin mai saboda Coronavirus

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya rage farashin man fetur a kasar sakamakon faduwar farshin man a kasuwar duniya saboda coronavirus.

    A wata sanarwa da karamin ministan man fetur Timipre Sylva ya fitar ranar Laraba, Buhari ya rage farashin ne domin 'yan Najeriya su amfana da faduwar farashin a kasuwar duniya.

    Ministan ya kuma bayar da umar ga hukumar kula da farashin man ta PPRA da bai wa kamfanin mai na NNPC da kuma 'yan kasuwa yadda sabon farashin zai kasance.

  8. Labarai da dumi-dumi, Coronavirus: Za a rufe makarantu a Kano da jihohin Arewa 6

    Gwamnonin jihohin arewa maso yammacin Najeriya sun ce za a rufe dukkan makarantu a jihohin saboda fargabar cutar coronavirus.

    Gwamnonin sun dauki matakin ne ranar Laraba bayan taron da suka gudanar a birnin Kaduna.

    Jihohin su ne Kano da Kaduna da Jigawa da Kebbi da Sokoto da Zamfara da kuma Katsina.

    Gwamna Badaru Abubakar na jihar Jigawa ya shaida wa BBC cewa suna sa ran rufe makarantun ranar Litinin mai zuwa bayan sun tattauna da hukumar shirya jarrabawar sakandare da takwararta ta share fagen shiga jami'a wato JAMB.

    "Za mu tattauna da hukumomin ne domin su ba mu shawara kan yadda za a bullo wa daliban da ke rubuta jarrabawar JAMB da kuma jarrabawar kammala sakandare wacce za a soma a watan Afrilu.

    "Ba ma so a rufe makarantun kuma ya shafi dalibai, shi ya sa muke son tattaunawa da wadannan hukumomi," a cewar Gwamna Badaru.

    Matakin gwamnonin yana zuwa ne bayan da ake zargin wani malamin jami'a ya kamu da cutar a jihar Katsina.

  9. Coronavirus: Abin da ya faru a yau zuwa yanzu

    • Fiye da mutum 200,000 ne suka kamu da coronavirus a fadin duniya tun bayan bullar cutar, kuma sama da 8,000 suka mutu.
    • Najeriya ta haramta wa 'yan kasashe 13 shiga kasar, wadanda cutar ta fi yi wa kamari, yayin da aka samu wasu mutum biyar sun kamu da cutar.
    • Cikin mutum biyar din da suka kamu har da wata mata da jaririyarta mai mako shida a duniya.
    • Mutum na farko ya mutu a Burkina Faso. Kasar ta sanar da mutuwar wata mata mai shekara 62 kuma mai ciwon suga.
    • Karin mutum biyu sun mutu a Masar: Dan kasar Masar mai shekara 70 da 'yar Italiya mai shekara 78 sun mutu a wani asibitin da aka kebe su.
    • Coronavirus ta shiga duka jihohin Amurka 50 bayan Jihar West Virginia ta bayyana rahoton bullar cutar a ranar Talata.
    • Mutum sama da 1,700 ne suka makale a kan wani babban jirgin ruwa a tekun Cape Town da ke Afirka ta Kudu sakamkaon fargabar wasu daga cikinsu na dauke da cutar coronavirus.
    • A Birtaniya an samu fiye da mutum 700 a cikin awa 24, jumulla sama da mutum 2,600 ke nan na wadanda suka kamu. Yankunan Scotland da Wales sun sanar da rufe makarnatu.
    • Kasar Spain ta rufe duka otel-otel a yakin da take yi da cutar musamman a birnin Madrid.
    • Kungiyar Tarayyar Turai ta fara aiwatar da haramcin shiga kasashen kungiyar daga wasu kasashen. Shugabannin kungiyar sun amince cewa shingen da wasu kasashe suka saka a cikin gida za a cire su.
    • Kazalika, iyakar kan tudu tsakanin Amurka da Canada - iyaka tsakanin kasashe biyu da ta fi kowacce girma a duniya - za a rufe ta. Babu karin bayani game da rufewar amma shugabannin kasashen biyu sun tabbatar da faruwar hakan.
    • Tsohon kyaftin din tawagar Super Eagles ta Najeriya John Mikel Obi ya bar kungiyar Trabzonspor bisa amincewar bangarorin biyu 'yan sa'o'i bayan ya ce ya kamata a soke wasanni a gasar Turkish Super Lig ta kasar Turkiiyya saboda coronavirus.
    • Spain za ta rufe otel-otel saboda coronavirus

      Gwamnatin kasar Spain ta tabbatar da cewa za ta rufe baki dayan otel a kasar daga ranar Talata 24 ga watan Maris, yayin da take ci gaba da yaki da cutar numfashi ta coronavirus.

      Sakamakon haka ne gwamnatin Birtaniya ta umarci 'yan kasarta da su fice daga Spain din kafin lokacin.

      A wani bayani, mai magana da yawun ofisahin jakadancin Birtaniyar ya ce matafiya a Spain su gaggauta tuntubar kamfanonin shirya tafiye-tafiye domin samun damar tafiya.

    • An kashe wani dan Kenya saboda coronavirus

      Wasu matasa sun yi wa wani mutum da ake zargin yana dauke da coronavirus duka har ya mutu a kudu maso gabashin Kenya.

      Shugaban 'yan sanda a yankin Nehemiah Bitok ya tabbatar wa BBC da mutuwar mutumin amma ya ce kawo yanzu ba a kama kowa kan kisan ba kuma ana ci gaba da bincike.

      Lamarin ya faru ne a kauyen Msambweni a gundumar Kwale, yankin gabar teku da masu yawon bude ido ke yawan ziyarta.

      Rahotanni sun nuna cewa an yi wa mutumin duka ne da misalin karfe 9 na daren Talata a hanyarsa ta komawa daga mashaya.

      Kawo yanzu ma'aikatar lafiyar Kenya ta tabbatar da kamuwar mutum bakwai a kasar.

      Kenya ta sanya tsauraran matakai kan baki kuma ta hana taron mutane don hana yaduwar cutar.

    • Coronavirus: Hana sallah a masallatai 'aikin addini' ne

      Rufe masallatai a wasu kasashe saboda coronavirus "aikin addini ne" duba da yadda cutar ta zama annoba ta duniya, in ji Mohammed Al-Issa sakataren kungiyar Muslim World League mai cibiya a garin Makka.

      "Wannan mataki na addini ne kamar yadda Shari'ar Musulunci ta tanadar. Kowa ya san cewa wannan annobar tana bukatar duk wani mataki na kare kai wanda ya hada da hana duk wani taron jama'a.

      "Shari'ar Musulunci ta shawarci wanda bakinsa yake wari bayan ya ci abinci da kada ya je sallar jam'i ballantana idan ya kamu da wata cuta mai hadari da ake gargadar mutane a kanta," Al-Issa ya bayyana.

      Saudiyya ta tabbatar da hana dukkanin salloli a masallatai a kasar, ban da masallatan harami guda biyu na Makka da Madina saboda a dakile yaduwar cutar ta coronavirus.

    • Zambia ta samu masu dauke da coronavirus a karon farko

      Zambia ta tabbatar da mutum biyu na farko da suka kamu da cutar Covid-19, wanda suka hada da wasu mata da miji da suka dawo daga Faransa.

      Ma'auratan sun je shakatawa ne tarea da 'ya'aynsu inda suka kwana goma, kuma hukumomi sun ce su killace kansu da suka dawo ranar lahadi.

      Duk cikinsu babu wanda ya nuna wasu alamun cutar amma gwajin da aka yi masu ya nuna suna dauke da cutar, kuma an yi masu gwajin ne saboda Faransa na da yawan cutar ta coronavirus.

    • Jaririya 'yar mako shida na cikin wadanda coronavirus ta kama a Najeriya

      Hukumar kare yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC ta ce cikin mutane biyar din da aka gano sun kamu da cutar coronavirus a Najeriya har da wata mata da jaririyarta mai mako shida a duniya.

      Sannan akwai wani dan Amurka, wanda ya shiga kasar ta tsandauri, inda ya kasance mutum na farko da ya shigo da cutar ba ta jirgin sama ba.

      Hukumar ta ce an tattara bayanai kan dukkan mutanen da zummar gano wadanda suka yi mu'amala da su.

      Ta yi kira ga 'yan Najeriya da su kwantar da hankalinsu yayin da jami'an kiwon lafiya ke daukar dukkan matakan da suka dace don yaki da yaduwar cutar a kasar.

      Kawo yanzu mutum takwas ne aka tabbatar suna dauke da cutar a Najeriya.

    • Labarai da dumi-dumi, Amurka ta rufe iyakarta da Canada

      Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa an rufe kan iyakar kasarsa da Canada na wani lokaci amma ban da ayyukan gaggawa.

      Trump ya wallafa a Twitter: "Bayan cimma matsaya tsakaninmu, za mu rufe iyakarmu ta arewa da Canada in ban da masu tafiyar gaggawa. Abin ba zai shafi kasuwanci ba. Akwai karin bayani."

    • Coronavirus: Mutum 1,700 sun makale a jirgin ruwa a Afirka ta Kudu

      Mutum sama da 1,700 ne suka makale a kan wani babban jirgin ruwa a tekun Cape Town da ke Afirka ta Kudu sakamkaon fargabar wasu daga cikinsu na dauke da cutar coronavirus.

      An fara nuna damuwa ne bayan daya daga cikin ma'aikatan jirgin da ya hau jirgin daga Turkiyya a ranar 9 ga watan Maris ya fara nuna alamun cutar.

      Tuni aka killace shi a cikin jirgin mai suna MV Corona tare da wani ma'aikacin da suka shigo jirgin sama daga Turkiyya tare.

      Bincike ya nuna cewa wasu mutum shida daga jirgin saman da suka hau sun shiga wani jirgin ruwa mai suna Aida Amira.

      Jirgin ruwan ya dauki hanya washegari, inda ya tsaya a Lüderitz da Walvis Bay na kasar Namibia kafin daga bisani ya koma Cape Town.

    • Labarai da dumi-dumi, Za a rika yin gwajin Coronavirus sau biyu a Ingila

      Daga yanzu za a rika gwajin cutar coronavirus sau biyu a Ingila.

      Za a kara kawo kayan aiki na haya domin kara yawan kayan aiki kan wadanda ma'aikatar lafiya ke da su a yanzu.

      A makon da ya gabata ne aka bayyana cewa za a kara yawan yin gwajin daga 2,000 a rana zuwa 10,000 ta hanyar amfani da dakunan gwaji na asibitoicin kudi domin tallafa wa asibitocin gwamnati.

    • Mikel Obi ya bar kungiyarsa bayan kalamansa kan Coronavirus

      Tsohon kyaftin din tawagar Super Eagles ta Najeriya John Mikel Obi ya bar kungiyar Trabzonspor bisa amincewar bangarorin biyu 'yan sa'o'i bayan ya ce ya kamata a soke wasanni a gasar Turkish Super Lig ta kasar Turkiiyya saboda coronavirus.

      Gasar Super Lig na daya daga cikin 'yan kalilan da ba su soke buga wasanni ba a Nahiyar Turai saboda yaduwar cutar, duk da cewa babu 'yan kallo ake buga wasannin.

      Mikel mai shekara 32, ya bayyana ra'ayin da ya ci karo da na hukumar a shafinsa na Instagram.

      A wani bayani da kulob din ya fitar ranar Talata ya ce dan wasan ya katse kwantaraginsa, sannan kuma ya hakura da albashinsa domin ya zama ba shi da kulob.

      A ranar Asabar ne Obi ya rubuta a Instagram "akwai sauran abbubuwa a rayuwa fiye da kwallon kafa, sannan ya ce: "Ba na sha'awa kuma ba zan buga wasa a irin wannan yanayin ba.

      "Ya kamata a ce kowa yana gida tare da iyalansa a wannan yanayin mai hadari. Ya kamata a dakatar da wasannin kakar bana yayin da duniya ke fuskantar tashin hankali."

      Ra'ayin na Mikel Obi ya jawo martani na goyon daga tsofaffin 'yan kwallon da suka taka leda a Turkiyya: Radamel Falcao wanda ya ce "haka yake John", sai kuma Didier Drogba da ya ce "tabbas ka yi hangen nesa".

      Mutanen da suka kamu da cutar a Turkiyya guda shida ne a lokacin da Mikel ya yi batun, duk da cewa yanzu sun kai 47.

    • Facebook zai yi yaki da labaran bogi kan coronavirus a Najeriya

      Facebook ya sanar da cewa zai fara wani sabon shiri na bin diddigi a Najeriya don taimakawa wajen hana yada labaran bogi kan coronavirus.

      Kamfanin na sada zumunta ya ce zai yi amfani da manhajarsa na Whatsapp don taimaka wa masu bincike tattara bayanan karya da kuma bayar da bayanan gaskiya.

      Ya kuma ce zai taimaka wajen samar da guraben yin talla ga Hukumar lafiya ta Duniya, WHO da Hukumar yaki da Yaduwar Cutuka a Najeriya, NCDC, don tallata bayanai kan coronavirus a kan Facebook a Najeriya.

      Hukumar bin-diddigi ta AfricaCheck za ta rika dubawa da karyata labaran da harsunan Yarabanci da Ibo da Hausa.

      Wannan dai na cikin matakan da kamfanin Facebook din ya dauka tare da wasu gwamnatocin kasashen Afrika don hana yada labaran karya ko kuma wadnda aka jirkita a shafukanta ciki har da Instagram.

    • Coronavirus: Wata mai ciwon suga ta mutu a Burkina Faso

      Burkina Faso ta sanar da mutuwar mutum na farko sanadiyyar COVID-19.

      Hukumomi sun ce wata mata ce mai shekara 62 kuma mai ciwon suga.

      "Wannan lamari ya nuna mana girman wannan matsalar da ke gabanmu," a cewar Martial Ouedraogo, mai jagorantar yadda kasashen Afrika ta Yamma ke yaki da coronavirus.

      "Wannan cuta ce da ake saurin dauk kuma take iya kashe mai dauke da ita, sannan kawo yanzu ba ta da magani."

      Burkina Faso ta tabbatar da mutum 26 da kamuwa da cutar.