Masarautar Kano tana cikin manyan masarautu a kasar Hausa a yammacin Afirka.
Tarihi ya nuna tsohuwar masarauta ce da aka kafa shekaru aru-aru tun zamanin jahiliyya kafin zuwan addinin Islama.
Masarautar ta taimaka wajen bunkasa garin Kano da Arewa da ma Najeriya baki daya.
Garin Kano ya kasance cibiyar kasuwanci a yankin arewacin Najeriya da Jamhuriyyar Nijar da ke makwabtaka da garin.
Mutanen da suka fara zama a Kano makera ne da suka tashi daga garin Gaya domin neman kasa mai arzikin tama, wacce za su sarrafa su yi karfe da ita.
Mutanen sun yi dace da samun kasar mai kunshe da sinadarin tama, sannan kuma mai albarkar noma da ruwa da dazuzzuka da za a iya yin farauta.
Wajen ya kuma kasance mai matukar tsaro kasancewar akwai manyan duwatsu da tsaunuka, da mutane za su iya hawa su fake idan an kai musu hari.
Duwatsun su ne dutsen Dala da Goron Dutse da Fanisau da Jigirya da Magwan.
Akwai kuma koguna daban-daban da suka kewaye yankin, da suka hada da kogin Jakara, da kuma kogin Kano.
Hakan ya sa mutane da dama suka ringa yin kaura zuwa yankin domin zama.
Karanta cikakken tarihin masarautar a nan.