An halaka mutum uku, bayan
wani harin makamin roka da aka kai kan wani sansani da dakarun Amurka da
Birtaniya ke zaune a Iraki.
A kalla mutum 12 aka raunata a
sansanin soja da ke Taji a arewacin Bagadaza.
Wasu majiyoyin sojan Amurka
sun ce, wani Ba’amurke dan kwangila da wani sojan Birtaniya sun rasa rayukansu
a harin. Sai dai ba a bayyana sunan kowa ba tukuna.
Ana cikin matukar zaman
dar-dar tun da Amurka ta kashe babban kwamandan Iran, Qasem Soleimani a wani
harin jirgin sama mara matuki da aka kai cikin watan Janairun da ya gabata.
Harin ramuwar gayya da Iran ta
kai al-Asad- wani sansanin da sojojin
Amurka ke zaune- a ranar 8 ga watan Janairu, ya bar sojoji fiye da 100 suna
fama da wasu lahanoni da suka shafi kwakwalwa.
Sai dai kuma da alamu Iran da
Amurka duka suna neman jan layi game da lamarin, kuma tun daga sannan babu wata
barkewar rikici.
Wani bayani da ya fito daga
rundunar hadin gwiwar da Amurka ke jagoranta a Iraki da Siriya, ta gasgata cewa
makaman roka 18 suka kai hari a sansanin, kuma an kashe jami’an rundunar
su uku.
Tun da farko wani sakon tuwita
da wani mai magana da yawun hadin gwiwar sojojin ya yada, ya ce harin ya auku
ne da karfe 7:35 na lokacin kasar (wato 4:35 agogon GMT) a ranar Laraba. Ya kara da cewa, an fara gudanar da bicike
kan lamarin.