Buhari ya nada kwamitin sasanta ’yan jam’iyyar APC

Asalin hoton, Nigeria Presidency
Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari tare da shugabancin jam'iyyar APC mai mulki sun kafa wani kwamiti da zai sasanta tsakanin 'ya'yan jam'iyyar.
Wata sanarwa da APC ta fitar ranar Litinin ta ce za a rantsar da kwamitin ranar Talata 11 ga watan Fabarairu a sakatariyar jam'iyyar da ke Abuja, da nufin lalubo hanyoyin magance korafe-korafen 'ya'yanta a fadin kasa baki daya.
Kwamitin yana da mambobi 12 kamar haka:
1. Chief Bisi Akande (Shugaba)
2. Gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello
3. Gwamnan Osun, Gboyega Oyetola
4. Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattijai, Sanata Yahaya Abdullahi
5.Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Ahmed Idris Wase
6. Sanata Umaru Tanko Al-Makura
7. Sanata Kashim Shettima
8. Karamar Ministar Muhalli, Sharon Ikeazor
9. Alh. Nasiru Aliko Koki
10. Sanata Khairat Gwadabe-Abdulrazak
11. Sanata Binta Garba
12. Sanata John Enoh (Sakatare)

















