Abubuwan da suka faru a Najeriya da Nijar da sassan duniya

Wannan shafin yana kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya and Nabeela Mukhtar Uba

  1. Sojojin Syria na gab da kwace ikon hanyoyin shiga manyan biranen kasar

    Rahotanni daga Syria na cewa sojojin gwamnatin kasar suna gab da kwace ikon manyan hanyoyin da ake amfani da su wajen shiga manyan biranen kasar hudu.

    Majiyoyin gwamnati sun ce babbar hanyar da ta doshi yankin da 'yan tawaye ke rike da shi a arewa-maso-yammacin Siriya nan da 'yan sa'o'i kadan sojoji za su kwace ikon wurin.

    Sojojin gwamnati da ke samun goyon bayan Rasha suna ta kai hare-hare a cikin watannin biyu da suka gabata, don sake bude hanyar da ta hada Damaskus da Aleppo.

    Akwai rahotannin da ke cewa 'yan tawayen da ke samun goyon bayan Turkiyya sun harbo wani jirgi mai saukar angulu mallakar gwamnatin Syria a wani waje da ke Idlib.

    Syria

    Asalin hoton, AFP

  2. An saki tubabbun 'yan 'Boko Haram' 1,400

    Gwamnatin jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya ta ce rundunar sojin kasar ta saki tubabbun mayakan kungiyar Boko Haram 1,400 sannan aka bar su suka shiga cikin jama'a.

    Jaridar PUNCH ta ambato kwamishinan watsa labarai na jihar, Babakura Jato, yana cewa an saki 'yan Boko Haram din ne kashi-kashi kuma a lokuta daban-daban tun da aka soma shirin ‘Operation Safe Corridor’.

    Ya kara da cewa ko da yake tun 2016 aka soma shirin, amma ba a fara sakar 'yan Boko Haram din ba sai 2018.

    Jato ya kara da cewa akasarin mutanen da aka saka ba cikakkun 'yan Boko Haram ba ne amma 'yan uwansu ne ko kuma mutanen da aka yi kuskuren kamawa.

    “Sau da dama ana sakarsu kashi-kashi. An sake su kashi uku. Kashin farko an sake su ne lokacin Gwamna There have been a series of releases. Shettima, yayin da sauran kashi biyu aka sake su lokacin mulkin Farfesa Zulum", a cewarsa.

    Mayakan Boko Haram

    Asalin hoton, Getty Images

  3. An kira taron kada kuri'ar amincewa da sabuwar gwamnati a Lebanon

    Hassan Diab

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dokoki a Lebanon ta kira wani babban taron kada kuri'ar amincewa da sabuwar gwamnati, duk da kokarin da masu zanga-zanga suke yi na hana taron ya gudana.

    Jami'an tsaro sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye kan daruruwan masu zanga-zangar a tsakiyar Beirut, wadanda ke kokarin hana 'yan majalisar shiga harabar majalisar.

    Gwamnatin, karkashin jagorancin sabon Firai Minista, Hassan Diab, ta gabatar da wata sanarwa game da manufofin da ke nuna cewa ana bukatar matakai masu zafi don magance matsalar rashin kudi da ta dabaibaye Lebanon.

  4. Sudan za ta mika tsohon Shugaba Omar al-Bashir ga ICC

    Hukumomin Sudan sun ce za su mika tsohon shugaban kasar Omar al-Bashir ga kotun hukunta masu aikata manyan laifuka.

    Tsohon shugaban kasar yana fuskantar zarge-zargen kisan kare-dangi, laifukan yaki da kuma na cin zarafin dan adam sakamakon yakin da ya barke a yankin Darfur a 2003.

    An hambarar da shi daga kan mulki a watan Afrilun 2019.

    Ya zama shugaban kasa ne bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a 1989 kuma an zarge shi da yin mulkin kama-karya.

    Omar al-Bashir

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, An zargi Omar al-Bashir da yin mulkin kama-karya.
  5. An bindige wadanda suka yi wa yarinya fyade

    Rundunar zartar da hukuncin kisa ta bindige wasu mutane biyu da aka samu da lafin yi wa wata yarinya 'yar shekara 12 fyade a arewa maso gabashin Somalia.

    A watan Fabrairun 2019 ne aka sace Aisha Ilyaas Aden, sannan aka kashe ta bayan an yi mata fyade a kusa da gidansu a garin Galkayo da ke lardin da ke ikirarin samun 'yanci na Puntland.

    Lamarin ya janyo zazzafar suka da zanga-zanga a fadin kasar.

    Tun da fari, an kama mutum 10 da ake zargi da hannu a yi wa yarinyar fyade amma wata babbar kotu ta samu mutum uku da laifi a watan Mayu.

    Masu shigar da kara sun ce sun gano masu laifin ne ta hanyar amfani da kwayoyin halittarsu.

    An harbe biyu daga cikinsu - Abdifatah Abdirahman Warsame da Abdishakur Mohamed Dige - a dandalin da ke garin Bossasso ranar Talata, a cewar jaridar Garowe da ake wallafawa a shafin intanet.

    An fasa kashe Abdisalam Abdirahman Warsame, wanda dan uwa ne ga Abdifatah, duk da cewa an yanke masa hukuncin kisa.

    Mahaifin Aisha, Ilyas Adan, ya shaida wa gidan talbijin na Puntland cewa shi ne ya bukaci kotu ta jinkirta kashe Abdisalam da kwana goma har sai an sake tantance lafinsa.

    Aisha Ilyaas Aden

    Asalin hoton, Radio Banaadir

  6. Mali ta fara tattaunawa da jagororin masu ikirarin jihadi

    Keita Mali

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Ibrahim Boubacar Keita ya shaida wa kafofin yada labaran Faransa cewa gwamnatinsa ta fara tattaunawa da fitattun masu da'awar jihadi da ke rura wutar rikici a kasarsa da ke yammacin Afirka.

    Wannan ne karo na farko da Keita ya tabbatar wa gwamnatinsa cewa yana tattaunawa da Iyad Ag Ghaly, shugaban reshen kungiyar al-Qaeda a yankin Sahel - Jamaat Nusrat al-Iskam wak-Muslimin (JNIM) da kuma Amadou Koufa, ''Bafulatani mai ikirarin kaifin kishin addini.''

    Ya shaida wa kafar yada labarai ta talbijin ta France 24 cewa: ''Wannan labari na sasantawa tsakanin Koufa da Lyad bai zo haka kawai ba... daga cikin mafitar da aka bayar a wajen taron zaman lafiya na kasa na baya-bayan nan har da batun sasantawar.

    ''Me zai hana mu yi kokarin tuntubar wadanda muka san suna kawo matsalar a Mali?''

    Ya ce tsohon shugaban rikon kwaryar kasar Dioncounda Traore ne wakilinsa a tattaunawar.

  7. An sake nada Sudais shugaban Masallatan Harami biyu tsawon shekara 4

    Sarki Salman na Saudiyya ya fitar da wata sanarwa ta tsawaita nadin Sheikh Abdul Rahman Al-Sudais a matsayin Shugaban masallatan Harami biyu na tsawon shekara hudu.

    Kafar yada labarai ta intanet ta Saudi Gazette ta ruwaito cewa Sudais ya yaba wa Sarki Salman da Yarima Muhammad Bin Salman saboda sake aminta da shi kan wannan matsayi yana mai cewa fadar na samun kulawa daga masu mulki.

    ''Wannan ya taimaka wa fadar wajen tafiyar da ayyukanta cikin sauki da kwarewa.

    ''Hakan kuma ya yi dai-dai da kulawa da kuma bibiyar harkokin tafiyar da Masallatan biyu masu tsarki da kuma masu ziyartarsu wanda ya ke biyan muradun jagoranci a kasar.''

    Sudais

    Asalin hoton, Saudi Gazette

  8. Babban Bankin Najeriya ya hana kudin shigo da madara kasar

    Babban bankin Najeriya, CBN, ya sanya madara da dangoginta cikin kayayyakin da ba zai bayar da rangwamen dala ga 'yan kasuwa domin siyo su a kasashen waje ba.

    Sai dai kuma bankin ya cire wasu kamfanoni shida daga cikin wadanda ya sanya wa wannan takunkumi.

    A cikin wata sanarwa da babban bankin ya wallafa a shafinsa na intanet, ya ce "A wani bangare na kokarin kara bunkasa samar da madara da dangoginta a Najeriya, CBN ya zabi wasu kamfanoni da za a horar da ma'aikatansu yadda za a rinka samar da madara a cikin gida mai kyau da karko."

    Babban bankin ya zabi wasu kamfanoni da su kadai aka lamuncewa shigo da madara da dangoginta wadanda suka hada da:

    Friesland Campina WAMCO Nigeria

    Chi Limited

    TG Arla Dairy Products Limited

    Promasidor Nigeria Limited

    Nestle Nigeria Plc (MSK only)

    Integrated Dairies Limited

    Wadannan kamfanoni da aka tsame daga cikin wadanda aka haramtawa shigo da madarar tuni suka fara samar da madarar gida a wani bangare na shirin inganta madarar gida da CBN din ya tsara.

    Tun a watan Yulin 2019, gwamnan babban bankin Godwin Emefiele, ya tabbatar da shirin su na haramta shigowa da madara da dangoginta domin bunkasa samar da madarar gida a kasa.

    Babban bankin Najeriya

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Babban bankin Najeriya cire kamfanoni shida daga cikin wadanda ya sanya wa wannan takunkumi
  9. 'Yan gudun hijirar Rohingya 14 sun mutu a hatsarin jirgin ruwa

    A kalla mutum 14 ne suka nutse a teku bayan da wani jirgin ruwa dauke da Musulman Rohingya 'yan gudun hijira ya kife a kudu da gabar tekun Bangladesh, in ji jami'ai.

    Jirgin na kan hanyarsa ta zuwa Malaysia ne kuma yana dauke da 'yan gudun hijirar Rohingya daga sansanonin Bangladesh, kamar yadda hukumomin kasar suka shaida wa BBC.

    Dukkan gawarwakin da aka samo zuwa yanzu duk mata ne da yara.

    Wani jami'i ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa kusan mutum 70 aka ceto.

    Sai dai har yanzu ba a ga wasu da yawa ba.

    Rohingya

    Asalin hoton, BANGLADESH NAVY

  10. Buhari ya yaba wa mata 'yan kwallon kwando

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yaba wa tawagar mata 'yan kwaloon kwando ta kasar, D’Tigress, saboda samun gurbin cancantar shiga gasar Olympics ta mata da za a yi a birnin Tokyo a 2020.

    Shugaban ya bayyana jin dadinsa kan nasarar da suka samu a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Litinin da almuru.

    Ya nemi 'yan tawagar kwallon kwandon su ci gaba da jajircewa sannan su fitar da kasar kunya a wurin gasar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  11. An rufe matatar man Libya saboda rashin danyen mai

    Kamfanin sarrafa albarkatun mai a Libya ya ce ya rufe wata matatar mai da ke yammacin kasar a ranar Litinin saboda rashin danyen mai.

    Kamfanin na NOC ya ce matakin ya biyo asarar fiye da dala biliyan daya da aka tafka sakamakon rufe wasu mahimman rijiyoyin mai da tashoshin mai.

    Matatar man ta Zawiya ta dakatar da harkokinta ranar Asabar bayan an rufe wani famfon mai da ke kan babban bututu tsakanin matatar da kuma filin mai na Sharara a hamada kudu maso yammacin kasar.

    Kamfanin na NOC cikin wata sanarwa ya ce rufewar za ta tsananta matsalar kula da shige da fice da kuma rarraba danyen man.

    Dakarun da ke goyon bayan Khalifa Haftar kuma suke da iko da akasarin yankunan da ke gabashi da kudancin Libya sun rufe bututan mai da tashoshin mai a Janairu abin da ya sa aka dakatar da samar da man tare da fitar da shi zuwa wasu kasashen.

    Oil

    Asalin hoton, Getty Images

  12. APC na gina wa kanta kabari a jihar Katsina - 'Ya'yan jam'iyya

    Wata kura da ta taso a jam'iyyar APC mai mulki a jihar Katsina na ci gaba da turnuke siyasar jihar.

    Al'amarin dai ya zo ne bayan wasu 'ya'yan jam'iyar sun yi ikirarin cewa APC na ginawa kanta kabari.

    Sun koka kan yadda suka ce jam'iyyar ta yi watsi da 'ya'yanta da suka yi wahala da ita tare da fifita wasu baki da suka kira su da tsoffin makiyan APC.

    Sai dai Uwar jam'iyyar ta musanta haka inda ta ce masu wannan zargi irin mutanen nan ne da gwamnatin jihar ta bai wa mukami amma suka raina, suka tafi Abuja saboda dogon buri.

    Bayanan sautiRahoton Rabi'a Kabir kan rikicin APC na Katsina
  13. Iran ta sa sojojin Amurka 109 sun samun ‘tabin hankali’

    Hukumomi a Amurka sun ce adadin sojin kasar da suka samu rauni a kwakwalwarsu bayan harin da Iran ta kai sansanin sojinsu da ke Iraq a watan Janairu ya kai 109.

    Wadannan alkaluma kari ne mai yawa a kan soji 64 da a baya hukumar tsaron Amurka ta Pentagon ta ce sun samu rauni sanadiyar harin.

    Tun da fari, Shugaba Donald Trump ya ce babu wani dan Amurka da ya ji rauni sakamakon harin.

    Harin, wanda aka kai shi ranar takwas ga watan Janairu, ya faru ne sakamakon rikicin da ya barke tsakanin kasashen biyu bayan Amurka ta hallaka kwamandan zaratan sojojin juyin-juya hali na Iran, Qasem Soleimani, a wani harin sama da sojojinta suka kai kan filin jirgin sama na Bagadaza, a Iraq.

    Kusan kasha 70 na sojojin da suke sansanin lokacin harin sun koma bakin aiki, in ji wata sanarwa da Pentagon ta fitar.

    Iran ta kai hari kan sansanin sojin Amurka ne domin yin ramuwar gayyar kashe Janar din sojin Iran Qasem Suleimani

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Iran ta kai hari kan sansanin sojin Amurka ne domin yin ramuwar gayyar kashe Janar din sojin Iran Qasem Suleimani
  14. Kashi 87 cikin 100 na matalautan Najeriya a Arewa suke - Bankin Duniya

    Wani rahoto da Babban Bankin Duniya ya fitar ya nuna cewa kashi 87 cikin 100 na matalautan da ke Najeriya suna zaune ne a arewacin kasar.

    Rahoton ya ce talauci a yankin kudu maso kudancin kasar ya yi gagarumar raguwa tsakanin 2011 da 2016.

    “Talaucin da ake fama da shi a arewacin kasar musamman a arewa maso yammaci yana ci gaba da karuwa.

    ''Kusan rabin matalautan mutane suna zaune ne a arewa maso yamma kuma kashi 87 na matalautan kasar na zaune ne a arewacin kasar," a cewar rahoton.

    Rahoton ya kara da cewa: “Talaucin da ake fama da shi a kudancin kasar bai wuce kashi 12 cikin 100 ba inda ake samun bambanci tsakanin yankunan da ke kudancin kasar.

    ''An samu raguwar talauci a yankin tsakanin 2011-2016."

    Kusan rabin matalautan mutane suna zaune ne a arewa maso yamma

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Kusan rabin matalautan mutane suna zaune ne a arewa maso yamma
  15. Atiku ya jinjina wa likitoci mata ‘yan gida daya

    Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar, ya jinjina wa wasu mata likitoci ‘yan gida daya.

    Daya daga cikinsu ne ta wallafa hotonsu su biyar inda ta ce mahaifinsu guda kuma dukkansu likitoci ne da suka kware a fannoni daban-daban.

    Da yake tsokaci a kan hoton, dan takarar shugabancin kasar a karkashin jam’iyyar PDP a zaben 2019, ya ce babu abin da ya fi dacewa ga al'umma fiye da bai wa mace ilimi.

    “Abin sha’awa ne. Idan ka bai wa mace ilimi, ka ilimantar da iyali da ma al’umma ne,” in ji Atiku.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  16. Ana yin jana’izar Daniel arap Moi

    Shugabannin kasashe 18 ne ake sa ran za su halarci jana’izar tsohon shugaban kasar Kenya Daniel arap, wadda ake yi ranar Talata a Nairobi, babban birnin kasar.

    Kazalika, dubban ‘yan kasar ta Kenya sun yi wa babban filin wasa na Nyayo tsinke domin yin bankwana da tsohon shugaban kasar.

    Mr Moi, wanda ya mutu ranar Talata yana da shekara 95 a duniya, ya kwashe shekara 24 yana jagorancin Kenya.

    Mr arap Moi ya dade yana jinya inda aka yi ta kwantar da shi a asibiti a lokuta daban-daban.

    Ko a watan Nuwambar 2019 an yi ta yada jita-jitar mutuwarsa amma daga bisani mai magana da yawunsa Mista Lee Njiru ya musanta.

    Shi ne shugaba na biyu da ya dade karagar mulki a Kenya tun bayan samun 'yancin kanta a 1963.

    arap Moi ya kwashe shekara 24 yana shugabancin Kenya

    Asalin hoton, Getty Images

  17. Buhari ya yi tur da hare-haren Boko Haram a Maiduguri

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jajanta wa iyalan mutanen da hare-haren Boko Haram ya rutsa da su a Maiduguri, babban birnin jihar Borno da ke arewa maso gabashin kasar.

    Shugaban ya bayyana haka cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai Garba Shehu ya fitar, inda ya ba su tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da fatattakar masu ta da kayarbayan har sai an ga bayansu.

    Ya kuma ce Boko Haram ''ta kusa zuwa karshe saboda dakaru na ci gaba da samun kayan aikin yaki da masu ta da tarzoma.''

    A cewarsa, ''gwamnatinsa za ta ci gaba da kokarin tabbatar da tsaron rayukan 'yan Najeriya, sannan hankalinta ba zai karkata ba saboda hare-haren da Boko Haram suke kai wa kan mutanen da ba su ji ba su gani ba.''

    Buhari

    Asalin hoton, Getty Images

  18. Aisha Buhari da Patience Jonathan sun gana kan siyasa

    Mai dakin shugaban Najeriya, Aisha Buhari, ta gana da matar tsohon shugaban kasar Patience Jonathan inda suka tattauna kan babutuwa da dama.

    Wata sanarwa da Aisha Buhari ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce Patience Jonathan ta kai mata ziyara a fadar shugaban kasar da ke Abuja ranar Litinin.

    “Mun tattauna kan yunkurina na ganin mata sun kara shiga harkokin siyasa da kuma gudanar da harkokin mulki a kananan matakai,” in ji Aisha Buhari.

    A makon jiya ma, mai dakin tsohon shugaban kasar, Turai Yar’adua ta kai ziyara wurin Aisha Buhari inda suka tattauna kan cin zarafin mata da shan miyagun kwayoyi.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  19. Barkanmu da warhaka

    Da fatan masu bibiyarmu a wannan shafi kuna nan lafiya. Muna kuma fatan za ku kasance tare da mu domin jin halin da duniya ke ciki, musamman Najeriya da Nijar da Kamaru da ma wasu sassan duniya.

  20. Sai da safenku

    Mun kawo karshen rahotannin kai-tsaye, sai kuma gobe da yardar Allah.

    Kafin nan, ku duba kasa domin karanta labaran ranar Litinin.