Kungiyar OIC ta yi watsi da shirin Trump na zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya

Asalin hoton, @OIC_OCI
Kungiyar hadin kan kasashen Musulmi ta Organisation of Islamic Cooperation (OIC) ta yi watsi da shirin zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya da Shugaban Amurka Donald Trump ya samar.
Kungiyar kuma ta yi kira ga kasashe mambobinta guda 57 da kada su taimaka wurin aiwatar da shirin.
Kungiyar ta bayyana hakan ne bayan wani taron ministocin harkokin wajen mambobinta da ta gudanar ranar Litinin a birnin Jeddah na Saudiyya, kamar yadda rahoton jaridar Saudi Gazette ya rawaito.
OIC wadda ke wakiltar Musulmi kusan biliyan 1.5 a fadin duniya, "ta yi watsi da wannan shiri na Amurka da Isra'ila saboda bai yi la'akari da mafi kankantar abin da Falasdinawa ke muradi ba da kuma hakkokinsu, sannan ya saba wa hanyoyin samar da zaman lafiya," in ji ta a wani bayani da ta fitar.
"Muna kira ga mambobin wannan kungiya da kada su taimaka ko kuma yin aiki tare da Amurka wurin aiwatar da shi ta kowacce irin hanya."
A karkashin shirin wanda Trump ya fitar a makon da ya gabata, Isra'ila za ta ci gaba da yin iko da birnin Kudus a matsayin babban birninta "nata ita kadai" sannan kuma ta mallaki wuraren da ta mamaye na Falasdinawa.
Trump ya ce za a bai wa Falasdinawa damar kafa babban birninsu a cikin yankin da Isra'ilar ta mamaye.
Saboda haka ne OIC ta jaddada goyon bayanta ga yankin gabashin Kudus a matsayin babban birnin kasar Falasdinu da za a samar nan gaba tare da nanata "alakarta da al'ummar Larabawa da kuma Musulunci".
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X

















