Yadda ake kula da masu fama da ciwon damuwa a Nijar
Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa masu fama da rashin lafiya da dama a kasar na fama da matsalar matsananciyar damuwa.
Kuma tuni hukumomi a kasar suka samar da kwararru a kan wannan fanni cikin asibitoci don taimaka wa masu fama da ciwon damuwa.
Wata Jami'a da ke kula da sashen masu fama da damuwa a wani babban asibiti da ke Yamai, babban birnin kasar Aishatu Bukar ta shaida wa BBC cewa suna ba da shawarwari ga mutanen da suke fama da wannan matsala.
Ta bayyana cewa ''muna bin masu fama da cutar sannu a hankali har sai an samar musu da mafita.''











