Isra'ila ta ce ta kashe kwamandan mayaƙan Hamas a Gaza
Sojojin Isra'ila sun ce sun kashe Fadi Fallah Ashour Daghmash, wanda suka bayyana a matsayin kwamandan sashen horaswa na rundunar mayaƙan Hamas, a wani hari ta sama da suka kai a arewacin Gaza.
A cikin wata sanarwa, sojojin Isra'ilar sun ce Daghmash ne ke jagorantar shirye-shiryen horas da mayaƙan Hamas, musamman rundunar ƙwararrunta.
Sun kuma zarge shi da jagorantar hare-haren da aka kai kan sojojin Isra'ila a Gaza, tare da cewa a cikin watannin baya-bayan nan yana ƙoƙarin sake farfaɗo da ƙarfin mayaƙan Hamas.
Sojojin Isra'ilar sun ƙara da cewa dakarunsu na ci gaba da kasancewa a yankin bisa yarjejeniyar tsagaita wuta, kuma za su ci gaba da kai hare-hare kan duk wata barazanar tsaro da suka ce tana tunkararsu.
Hamas dai ba ta fitar da wata sanarwa da ke tabbatar ko musanta ikirarin na Isra'ila ba.












































