An ga watan azumin Ramadan na 2022 a Najeriya

wata

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Kwamitin duban wata a Najeriya ya sanar da cewa an ga watan azumin Ramadan na shekarar 2022 a wasu sassan ƙasar.

Hakan na nufin a ranar Asabar 2 ga watan Afrilun 2022 za a tashi da azumin a matsayin 1 ga watan Ramadan na shekarar 1443 bayan Hijira.

Sanarwar ta Najeriya ta zo ne bayan da ƙasar Saudiyya ta sanar da nata ganin watan tun da yammacin 1 ga watan Afrilun, wato sa'o'i kadan kafin ganin na Najeriya.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Kwamitin ganin watan wanda ya wallafahakan a shafina na Tuwita ya ce an gan shi ne a garuruwan Bauchi da Gombe da Azare da Misau da Numan da Legas da Kaduna da Abuja da Bajoga da Nafada da kuma birnin Maiduguri da wasu da dama.

A can Jamhuriyar Nijar ma rahotanni sun ce an sanar da ganin watan azumin.