Fitaccen marubuci kuma ɗan wasan Hausa Kasagi ya rasu
An wallafa
Latsa hoton da ke sama domin kallon hirar da muka yi da shi kwanakin baya:
Fitaccen marubuci kuma ɗan wasan kwaikwayo na Hausa, Alhaji Umaru Ɗanjuma wanda aka fi sani da Kasagi, ya rasu.
Ya rasu ne a birnin Katsina da ke arewacin Najeriya ranar Juma'a.
Marigayin ya yi fice a fannin rubutun Hausa da wasan kwaikwaiyo, kusan a iya cewa su ne na farko-farko a ƴan wasan Hausa.
Haka kuma, shi ya rubuta sanannen littafin Hausa na Kulɓa Na Ɓarna.
An haife shi ya birnin Katsina a shekarar 1950.
Ya yi karatu a Najeriya da Ingila, inda ya ware a fannin fina-finai.
Ya bar mata biyu da 'ya'ya 13.










