Fitaccen marubuci kuma ɗan wasan Hausa Kasagi ya rasu

Bayanan bidiyo, Umar Danjuma Katsina
An wallafa

Latsa hoton da ke sama domin kallon hirar da muka yi da shi kwanakin baya:

Fitaccen marubuci kuma ɗan wasan kwaikwayo na Hausa, Alhaji Umaru Ɗanjuma wanda aka fi sani da Kasagi, ya rasu.

Ya rasu ne a birnin Katsina da ke arewacin Najeriya ranar Juma'a.

Marigayin ya yi fice a fannin rubutun Hausa da wasan kwaikwaiyo, kusan a iya cewa su ne na farko-farko a ƴan wasan Hausa.

Haka kuma, shi ya rubuta sanannen littafin Hausa na Kulɓa Na Ɓarna.

An haife shi ya birnin Katsina a shekarar 1950.

Ya yi karatu a Najeriya da Ingila, inda ya ware a fannin fina-finai.

Ya bar mata biyu da 'ya'ya 13.