Gabriel Jesus ya gama buga Gasar Kofin Duniya a Qatar

Gabriel Jesus

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa

An yi wa dan kwallon Arsenal, Gabriel Jesus tiyata cikin nasara, hakan na nufin ya gama buga wa Brazil Gasar Kofin Duniya da ake yi a Qatar.

Mai shekara 25 tare da Alex Telles sun ji rauni a wasan karshe a rukuni da Kamaru ta ci 1-0 ranar Juma'a.

Wasan da aka fara da shi kenan a babbar Gasar tamaula ta Duniya a Qatar, bayan da ya canji dan wasa a karawa da Switzerland da kuma Serbia a rukuni.

Arsenal ta sanar da cewar dan kwallon ya fara jinya, sai dai ba a fayyace ranar da zai koma taka leda ba, illa dai ya gama buga wasannin da ake yi a Qatar.

Jesus ya ci wa Arsenal kwallo biyar a dukkan karawar da ya yi mata a bana, bayan da ya koma Emirates daga Manchester City.

Brazil za ta kara da Croatia a wasan Quarter finals ranar Juma'a 9 ga watan Disamba, bayan da ta ci Koriya ta Kudu 4-1 ranar Litinin a wasan zagaye na biyu.

Croatia ta kai daf da na kusa da na karshe, bayan da ta ci Japan 3-1 a bugun fenariti, sakamakon da suka 1-1 a minti na 120 ranar Litinin.