Mutum sama da miliyan daya sun kamu da coronavirus a duniya

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a duniya baki daya dangane da annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Awwal Ahmad Janyau, Usman Minjibir and Umar Mikail

  1. Rundunar sojin Najeriya ta dauki matakai kan Covid-19

    Rundunar sojin Najeriya ta ce ta dauki matakai daban-daban a bariki-bariki 19 da ke fadin kasar domin hana yaduwar cutar coronavirus.

    Sanarwar da mai magana da yawun rundunar, Kanar Sagir Musa, ya aike wa manema labarai ranar Talata ta ce matakan da ta dauka sun hada da samar da abubuwan wanke hannu da man wanke hannu na sanitizer da kuma auna yanayin zafin jikin ma'aikatanta a bariki-bariki.

    "Alal misali, hedikwatar rundunar soji wacce ke kulawa da lafiya da ke Victoria Island Lagos ta dauki matakai domin dakile cutar kamar yadda hafsan sojin kasa Laftanar Janar Tukur Yusufu Buratai ya yi umarni.

    Ma'aikatan lafiya a Bonny Cantonment sun zage dantse wurin tantance mutanen da ke shiga da fita daga bariki ta hanyar gwada yanayin zafin jikinsu da kuma tabbatar da cewa sun wanke hannuwansu da zummar hana kamuwa da cutar," in ji Kanar Musa.

    Sanarwar ta kara da cewa rundunar za ta ci gaba da tabar da tsaftar jami'anta da sauran ma'aikata a yunkurin hana kamuwa da coronavirus.

    Sojoji

    Asalin hoton, Nigeria Army

    Sojoji

    Asalin hoton, Nigeria Army

  2. Labarai da dumi-dumi, Karin mutum hudu sun kamu da coronavirus a Najeriya

    Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a Najeriy, NCDC, ta ce an samu karin mutum hudu da suka kamu da coronavirus a kasar.

    A sakon da ta wallafa a Twitter ranar Talata, NCDC ta ce uku daga cikin mutanen daga Osun suke yayin da daya yake daga Ogun.

    Ya zuwa yanzu ana da jumullar mutum 135 da suka kamu da cutar a Najeriya.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  3. Labarai da dumi-dumi, Coronavirus ta yi illar da bata taba yi ba cikin kwana daya a Spain

    An samu karin mutum 849 da suka mutu sakamakon coronavirus a Spain, inda ya kasance ma fi yawa da aka samu cikin kwana daya a kasar tun bullar cutar.

    Ma'aikatar lafiyar kasar ta ce yanzu mutanen da suka mutu sun kai 8,189 jumulla.

    Spain ce kasar da cutar ta fi yi wa illa a Turai bayan Italiya.

  4. Coronavirus: Titunan Abuja sun zama tamkar kufai

    Titunan Abuja, Babban Birnin Tarayyar Najeriya sun zama tamkar kufai bayan da a ranar Talata, dokar da shugaban kasar Muhammadu Buhari ya sanya ta hana fita ta soma aiki.

    A jawabin da shugaban ya yi a karshen makon jiya, ya umarci a rufe biranen Abuja da Lagos da kuma Ogun zuwa mako biyu a wani matakin hana yaduwar coronavirus.

    Ya zuwa yanzu dai mutum 131 ne suka kamu da cutar a Najeriya, 25 daga cikinsu a Abuja.

    Abuja ta zama fayau
    Abuja ta zama fayau
    Abuja ta zama fayau
    Abuja ta zama fayau
    Abuja ta zama fayau
    Abuja ta zama fayau
  5. 'Yan fansho sun mutu a layin karbar tallafi

    'Yan fansho biyu a Afirka ta Kudu sun mutu ranar Litinin a yunurinsu na karbar tallafi daga wurin gwamnatin kasar.

    Rahotanni su ce mutum na farko ya mutu ne a kan layin karbar tallafin a Hammersdale, wajen birnin Durban, yayin da dayan ya mutu a cikin motar tasi a kan hanyarsa ta zuwa na'urar ATM domin ya cire kudin a lardin Pimville, kusa da Johannesburg.

    Hukumomi basu bayyana sunayen mutanen ba.

    Jaridar Daily Sun ta ambato ministar walwalar jama'a Lindiwe Zulu tana cewa "Muna mika ta'aziyyarmu ga iyalai da abokan mutanen da suka rasu."

    Ta bukaci a biya su tallafinsu nan take "ba tare da bata lokaci ba".

    A halin da ake ciki Afirka ta Kudu an rufe tsawon mako uku a yayin da hukumomi ke kokarin hana yaduwar coronavirus wacce ya zuwa ta kama mutum 1,300, sannan mutum uku suka mutu.

    Taswirar Afirka ta Kudu

    Asalin hoton, Getty Images

  6. Ministan Abuja 'ba ya dauke da coronavirus'

    Ministan Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, Mohammed Musa Bello ya ce ba ya dauke da cutar covid-19.

    A jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na Twitter, ranar Talata, ministan ya ce gwajin da aka yi masa na cutar ya nuna cewa kalau yake.

    "Na gode. Ina kira a gare ku da ku yi biyayya ga dookin da aka gindaya muku domin ku tsira daga harbuwa da covid-19," a cewar ministan.

    A makon jiya ne takwararsa a ma'aikatar Birnin Tarayya, Hajiya Ramatu Tijjani Aliyu, ta ce ita ma ba ta dauke da cutar bayan da aka yi mata gwaji.

    Ya zuwa yanzu dai, mutum 25 aka tabbatar sun kamu da coronavirus a Abuja.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  7. Coronavirus: Somalia ta rufe makarantun allo

    Gwamnatin Somalia ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun Islamiyya da na allo a kokarinta na dakile yaduwar coronavirus.

    Ta bukaci mutane su yi sallah a gida tsawon mako biyu maimakon zuwa masallatai.

    Ko da yake ya zuwa yanzu mutum uku ne suka kamu da coronavirus a Somalia, ana fargabar cewa kasar ba za ta iya dakile cutar ba.

    Asibitocin kasar sun kwashe shekara 30 suna bayar da magani ga mutanen da yaki ya tagayyara inda kuma miliyoyin mutane suka koma sansanonin 'yan gudun hijira makare da jama'a.

    Kungiyar al-Shabab, wacce ke iko da akasarin kudanci da tsakiyar Somalia, ta ce "kafirai" ne kawai za su kamu da Covid-19, tana mai cewa su ne ma'aikatan gwamnati da hukumomin kasashen waje.

    An bukaci mutane su yi sallah a gida na mako biyu maimakon zuwa masallatai.

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, An bukaci mutane su yi sallah a gida na mako biyu maimakon zuwa masallatai
  8. Amurka za ta kwashe jami'anta daga Najeriya saboda coronavirus

    Amurka za ta kwashe jami'anta daga biranen Lagos da Abuja da ke Najeriya bayan gwamnatin kasar ta sanya dokar hana fita ta mako biyu a yunkurinta na dakile yaduwar coronavirus.

    Ofishin jakadancin Amurka da ke kasar ya wallafa sakon Twitter da ke cewa jiragen gaggawa za su kwashe 'yan kasarta daga biranen biyu a wannan makon.

    Za a tuntubi mutanen da za a kwashe kai tsaye kuma ofishin jakadancin ya shawarci dukkan 'yan kasar ta Amurka da ke Najeriya su shirya tsaf kafin a tuntube su

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    A rufe kasuwanni da sauran wurare

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, A rufe kasuwanni da sauran wurare
  9. Covid-19 ta kashe tsohon shugaban kasar Congo

    Tsohon shugaban kasar Jamhuriyar Dimokradiyar Congo, Jacques Joaquim Yhombi-Opango, ya mutu a birnin Paris sakamakon cutar coronavirus.

    Ya mutum yana da shekara 81 a duniya. Iyalansa sun ce da ma yana fama da rashin lafiya kafin ya harbu da coronavirus.

    Mr Yhombi-Opango ya shugabancin Congo-Brazzaville daga 1977 har lokacin da shugaban da ke mulki yanzu Denis Sassou Nguesso ya kifar da gwamnatinsa a 1979.

    Ya kwashe shekaru da dama a gidan yari kafin a kaddaar da tsarin jam'iyyu da dama a 1991 inda ya zama firai minista har zuwa lokacin da yakin basasa ya barke a 1997.

    Ya tafi gudun hijira a kasar Faransa, ko da yake an kyale shi ya koma kasarsa shekara 10 bayan haka.

    Iyalansa sun ce da ma yana fama da rashin lafiya kafin ya harbu da coronavirus

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Iyalansa sun ce da ma yana fama da rashin lafiya kafin ya harbu da coronavirus
  10. Coronavirus: Wanne hali duniya ke ciki?

    Alkaluman da cibiyoyin da ke bibiyar coronavirus suka fitar ranar Talata sun nuna cewa cutar na ci gaba da mamaye duniya.

    Jami'ar Johns Hopkins ta Amurka, wacce ke bayar da bayanai dalla-dalla game da cutar ta ce ya zuwa ranar Talata da safe, fiye da mutum 787,000 ne suka kamu da ita.

    A cewarta, sama da mutum 166,000 sun warke yayin da fiye da mutum 37,000 ne suka mutu.

    Ga jerin kasashe goma da suka fi fama da cutar:

    Amurka - 164,610

    Italiya - 101,739

    Spain - 87,956

    China 82,240

    Jamus - 66,885

    Faransa - 45,170

    Iran - 41,495

    Birtaniya - 22,454

    Switzerland - 15,922

    Belgium - 11,899

    Coronavirus

    Asalin hoton, AFP

  11. Farawa

      • Marubuci, Nasidi Adamu Yahya
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hausa, Abuja

    Nasidi Adamu Yahaya ne yake yi muku barka da wannan safiya.

    Da fatan za ku kasance tare da mu domin sanin halin da duniya ke ciki game da annobar coronavirus da ma wasu labarai da rahotanni na daban.

    Za mu fi mayar da hankali ne kan labaran Najeriya da Nijar da wasu kasashen Afirka, har ma da sassan duniya.

    Kada ku manta za ku iya takfa muhawara da bayyana ra’ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta da muhawara.

  12. Rufewa

    Masu bibiyarmu nan muka kawo karshen shirin namu da ke kawo muku bayanai kai tsaye dangane da abubuwan da ke wakana dangane da annobar coronavirus da ke addabar duniya. Da fatan za ku kasance da mu gobe da safiyar Talata. Allah ya tashe mu. Ya kuma kare mu daga sharrin wannan annoba.

  13. Labarai da dumi-dumi, An kara samun mutum 20 da suka kamu da coronavirus a Najeriya

    Hukumar da ke hana yaduwar cututtuka ta Najeriya, NCDC ta ce an kara samun sabbin mutum 20 da suka kamu da coronvirus a kasar.

    Hukumar ta ce mutum 13 daga cikinsu a jihar Legas ne , inda 4 suka fito daga Abuja da kuma 2 daga jihar Kaduna sai kuma 1 daga jihar Oyo.

    Yanzu haka Najeriya na da jumullar mutanen da suka kamu da cutar ta coronavirus 131 a fadin kasar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  14. Coronavirus: Italiya ta tsawaita dokar kulle zuwa 12 ga Afrilu

    Ministan lafiya na kasar Italiya ta sanar da tsawaita dokar kulle har zuwa ranar 12 ga watan Afrilu.

    Wannan dai na zuwa a dai-dai lokacin da alkaluman mutanen da suka mutu suka daga zuwa 11,591.

    Italiya dai ta sa dokar kulle ta makonni uku da suka wuce.

  15. An gurfanar da fasto a gaban kuliya kan karyata cutar coronavirus

    Uganda

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a Uganda na tuhumar fasto bisa zargin shaida wa mabiyansa cewa babu cutar coronavirus a nahiyar Afirka.

    Masu gabatar da kara na gwamnati na zargin fasto Augustine Yiga na cocin Revival Christian Church congregation da yin wasu kalaman iza mabiya a gidajen talbijin na kasar.

    Fasto Augustine Yiga dai ya musanta zarge-zargen.

    Idan dai an kama fasto Augustine da laifi to zai fuskanci zaman gidan yari na shekara bakwai.

    Uganda dai na da mutum 33 masu dauke da cutar coronavirus.

  16. Mohammadou Issoufou ya yi wa Hamma Amadou afuwa

    Issoufou

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban jamhuriyar, Niger, Mahammadou Issoufou ya yi wa fursunoni 1500 da ke gidajen yarin kasar afuwa, ciki har da jagoran hamayyar kasar da ke tsare Hamma Amadou.

    Babu tabbas cewa ko shugaban ya yi hakan ne da manufar rage cinkoson da ke gidajen yarin kasar kamar yadda wasu kasashe ke yi a wannan zamani na annobar coronavirus.

    Kawo yanzu dai mutum 22 ne suke dauke da cutar a jamhuriyar ta Niger, inda mutum suka rasu.

  17. Za a daure wani da ya tofa wa 'yan sanda yawu a Birtaniya

    .

    Asalin hoton, NOTTINGHAMSHIRE POLICE

    An yanke hukuncin daurin shekara daya ga wani mutum da ya tofa wa 'yan sanda yawu a Birtaniya.

    Paul Leivers, ya yi ikirarin yana dauke da cutar coronavirus kuma ya amince da laifukan da ake zarginsa da su.

    'Yan sanda a Nottinghamshire sun tabbatar da cewa mutumin bai dauke da coronavirus kuma 'yan sandan da aka tofa wa yawun na nan cikin koshin lafiya.

  18. Labarai da dumi-dumi, Gwamnan Oyo ya kamu da coronavirus

    .

    Asalin hoton, @seyiamakinde

    Gwamnan jihar Oyo Seyi Makinde ya kamu da cutar coronavirus.

    Gwamnan ne ya bayyana haka a wasu jerin sakonni da ya wallafa a shafinsa na Twitter.

    A halin yanzu ya bayyana cewa ya killace kansa.

    Ko a kwanakin baya sai da gwamnonin Bauchi da Kaduna suka bayyana cewa sun kamu da cutar ta coronavirus.

  19. Ganduje ya kama motocin da suka yi yunkurin shiga Kano

    .

    Asalin hoton, @dawisu

    Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya kama wasu motoci da suka yi yunkurin shiga Kano.

    Ciki har da wata babbar mota cike da mutane da ke niyyar shiga jihar.

    A makon da ya gabata ne gwamnatin jihar ta Kano ta dakatar da shiga da fita garin a yunkurinta na dakile yaduwar cutar coronavirus.

    Gwamnan da kansa ya raka motocin da ya kama zuwa ofishin 'yan sanda ma fi kusa, kamar yadda mai taimaka wa gwamnan kan kafofin sadarwa na zamani Salihu Tanko Yakasai ya wallafa a shafinsa na Twitter.

    .

    Asalin hoton, @dawisu

  20. Labarai da dumi-dumi, Covid-19: Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutum na biyu

    Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutum na biyu wanda coronavirus ta kashe a kasar.

    Ministan Lafiya na kasar Dakta Osagie Ehanire ne ya tabbatar da hakan a ranar Litinin a Abuja.

    Sai dai ministan bai tabbatar da mutuwar ko mace ce ko namiji bane da kuma jihar da aka yi mutuwar.

    Ya bayyana cewa zuwa yanzu an sallami mutum uku wadanda suka warke sakamakon cutar.

    Ko a dazu sai da gwamnatin jihar Legas ta ce za a sallami karin mutum biyar da suka warke daga cutar coronavirus.