Mutum sama da miliyan daya sun kamu da coronavirus a duniya

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a duniya baki daya dangane da annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Awwal Ahmad Janyau, Usman Minjibir and Umar Mikail

  1. Coronavirus: Tarayyar Afirka ta ce mutum 387 suka warke a Afirka

    Tarayyar Afirka ta ce mambobinta 48 sun bayar da rahoton jimillar mutum 5,413 da ke dauke da cutar coronavirus a nahiyar.

    A sanarwar da ta fitar a Twitter ta ce adadin mutum 172 suka mutu sanadiyar cutar, yayin da kuma mutum 387 suka warke.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. Tattaunawa da Farfesa Sheikh Ibrahim Maqri kan annobar Coronavirus.

  3. Coronavirus: Wadanda suka mutu a Amurka sun zarce 3,000

    Alkalumman hukumomin Lafiya a Amurka sun ce yawan wadanda cutar coronavirus ta kashe sun haura mutum 3,000.

    Adadin ya zarce yawan wadanda suka mutu a harin 11 ga wantan Satumban 2011 inda kusan mutum 3,000 suka mutu.

    Shugaba Trump

    Asalin hoton, Getty Images

  4. Gwamnatin Legas na raba wa mutane kayan abinci

    Gwamnatin jihar Legas ta fara raba kayayyakin abinci ga mazauna jihar da aka hanawa fita domin gudun bazuwar cutar Coronavirus.

    Wakilin BBC a Legas y ace tun kafin dokar hana fita a biranen Legas da Abuja da Ogun ta fara aiki ne, gwamnatin ta Legas ta fara raba kayan abincin

    Sai dai kuma ta ce akwai wasu daga cikin al'ummar jihar da ke fargabar cewa tallafin ba zai iso gare su ba inda wasunsu suka bukaci a sa ido sosai don gudun kada wasu su karkatar da tallafin.

    Bayanan sautiGwamnatin Legas na raba wa mutane kayan abinci
  5. Coronavirus: Halin da ake ciki a China yanzu

    China

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Hoton wani bikin aure kenan a kasar China da aka yi ranar 29 ga watan Maris 2020

    Yanzu haka an sassauta dokokin kulle da na hana fita a China, kasar da a can ne annobar coronavirus ta fara bayyana a karshen 2019.

    Mutane da gudanar al'amuransu a kan tituna kamar yadda aka saba a baya kafin bullar cutar duk da cewa ana gwada yanayin zafin jikinsu sannan kuma har yanzu jama'a na sanya takunkumin kariya.

    Sashen BBC na duniya ya tattauna da wasu 'yan kasar a birnin Beijing da Shangai dangane da yadda suke gudanar da rayuwa, inda suka ce hankalinsu ya kwanta amma dai suna ci gaba da daukar matakan kariya.

  6. Coronavirus: An samu wasu mutane boye a bayan babbar mota a Pakistan

    Pakistan

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla mutum 50 aka aike da su cibiyoyin killace jama'a a Pakistan bayan samun su a boye a cikin kontena da ke bayan wata babbar mota a Pakistan.

    An dai gano mutanen ne a a cikin kontenar a yankin Chiniot da ke lardin Punjab mai nisan fiye da kilomita 1000 daga birnin Karachi daga inda babbar motar ta tashi.

    Duk da cewa ba a hana shigar kayan abinci zuwa wurare ba, amma sai da aka binciki motar bisa zargin tana dauke da mutanen a cikinta.

  7. An yi garambawul a rundunar sojan Najeriya

    Rundunar sojin Najeriya ta yi garanbawul ga janar-janar da wasu manyan jami'anta.

    Sanarwar da mai magana da yawun rundunar, Kanar Sagir Musa, ya aike wa manema labarai ranar Talata ta ce an yi garanbawul din ne domin inganta yadda jami'anta suke gudanar da ayyukansu.

    Manyan sauye-sauyen da aka yi sun hada da - nadin da aka yi wa Manjo Janar ACC Agundu daga Sashen Runduna ta Musamman ta SAFE HAVEN Jos zuwa Nigerian Army Resource Centre (NARC) Abuja a matsayin Babban Jami'i; Manjo Janar HI Bature daga reshen Hedikwatar Tsaro da ke Majalisar dokokin Najeriya zuwa Army Headquarters Department of Civil Military Affairs inda aka nada shi a matsayin Chief of Civil-Military Affairs.

    Kazalika an sauya wa Manjo Janar UM Mohammed wurin aiki daga Nigerian Army Property Limited (NAPL) zuwa ofishin Hafsan sojan kasa inda aka ba shi mukamin mai bayar da shawara na musamman na Jami'ar sojin kasa da ke Biu/Mataimakin shugaban kwamitin amintattu na NAPL, yayin da tsohon mai bayar da shawara na musamman na Jami'ar sojin kasa da ke Biu Manjo Janar CC Okonkwo yanzu ya koma STF Operation SAFE HAVEN Jos inda ya zama Kwamanda.

    Laftanar Janar Y.T Buratai

    Asalin hoton, HQ Nigerian Army

  8. Coronavirus: Legas ta sallami mutum 5 da suka warke

    Gwamnatin jihar Legas a Najeriya ta salami mutum biyar da suka warke daga cutar coronavirus.

    Sanarwar da ta fitar a Twitter, ma’aikatar lafiya ta jihar ta ce mutanen sun kunshi mace daya da maza hudu da aka sallama.

    Ta ce yanzu jimillar mutum 8 aka sallama kenan da suka warke daga cikin wadanda aka killace a asibitin kula da cututuka masu yaduwa a Yaba inda ake kula da masu rashin lafiyar cutar coronavirus.

    Sai dai hukumar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC ba ta tabbatar da warkewar tasu ba.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  9. Coronavirus ta kashe karin mutum 393 a Burtaniya

    An kara samun mutum 393 da suka mutu sakamakon cutar coronavirus a Burtaniya.

    Yanzu haka mutum 1,801 ne suka mutu sakamakon kwayar cutar a fadin kasar, da suka hada da 367 a Ingila, 13 a yankin Scotland da kuma bakwai a Wales sannan 6 a Northern Ireland

  10. Coronavirus: 'Yan sanda sun harbe yaro dan shekara 13 a Kenya

    Kenya

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban 'yan sanda a kasar Kenya ya bayar da umarnin yin bincike dangane da kisan wani yaro dan shekara 13 da aka harbe da yammacin Litinin a lokacin da jami'an 'yan sandan kasar ke kokarin tabbar da an bi dokar hana fita.

    Yaron dai na wasa ne a saman benen gidansu da ke wata unguwar marasa galihu a wajen birnin Nairobi, lokacin da 'yan sanda suka yi harbin kan mai uwa da wabi domin tarwatsa jama'a.

    An dai harbin yaron ne a cikinsa inda daga bisani ya rasu a a lokacin da yake karbar magani a asibiti.

  11. Coronavirus 'za ta jefa mutum milyan 24 cikin talauci'

    IMF

    Tasirin coronavirus ga hada-hadar kudi zai jefa kusan mutum miliyan 24 a talauci, a kasashen gabashin Asiya da na Pacific, a cewar Bankin Duniya.

    Bankin ya bayyana cewa ''za a samu matsin tattalin arziki a duka kasashen duniya''.

    Bankin Duniyar ya yi gargadi kan jama'ar da suka dogara kan masana'antu da cewa suna cikin babban hatsari sakamakon tasirin da cutar za ta yi.

    Cutar za ta yi tasiri ga yawan bude ido a Thailand da Tsibirin Pacific, da kuma wasu kamfanoni da ke a Vietnam da Cambodia.

    Bankin ya bukaci yankunan da su kara inganta bangaren kiwon lafiya da kuma kayayyakin aiki, tare da bayar da tallafi ga marasa lafiya.

    A wani hasashe da ya yi, bankin ya ce idan abubuwa ba su tabarbare sosai ba kusan mutum miliyan 24 za su tsallake fadawa talauci a yankin a 2020, sakamakon tasirin da annobar za ta yi ga tattalin arziki.

    Idan kuma abubuwa sun tabarbare matuka kamar yadda bankin ya yi hasashe, kusan mutum miliyan 35 za su kasance cikin talauci, ciki har da mutum miliyan 25 a China.

  12. Dokar hana fita a Abuja ta yi tasiri

    Titunan birnin Tarayyar Najeriya Abuja sun kasance wayau ba motoci, yayyin da a wasu unguwanni kamar an yi ruwa an dauke.

    Sai dai duk da manufar dokar hana fita ita ce dakile yaduwar cutar coronavirus, amma yara ne ke amfani da damar domin wasan kwallon kafa a titunan unguwanninsu.

    Bayanan bidiyo, Coronavirus: Yadda Yara ke kwallo a wasu titunan Abuja
  13. Coronavirus: ‘Yan majalisar wakilan Najeriya sun sadaukar da albashinsu na wata biyu

    ‘Yan majalisar wakilan Najeriya sun sanar da matakin sadaukar da daukacin albashinsu na tsawon wata biyu a matsayin tallafi ga yakin da kasar ke yi da cutar Covid 19.

    Cikin wani sakon bidiyo ga 'yan Najeriya da ya wallafa a Twitter, Kakakin majalisar Femi Gbajabiamila ya ce mambobin majalisar wakilai 360 ne suka yanke shawarar sadaukar da albashinsu na wata biyu.

    Ya ce albashin na wata biyu, na a matsayin tallafi ne ga ‘yan Najeriya domin rage radadin wahalar da mazabunsu ke fuskanta a wannan lokaci na dokar ta-baci.

    Kauce wa X, 1
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X, 1

    Kauce wa X, 2
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X, 2

  14. Coronavirus: NAFDAC ta amince a samar da maganin chloroquine

    NAFDAC

    Asalin hoton, NAFDAC's Twitter

    Hukumar kula da ingacin abinci ta magunguna ta Najeriya NAFDAC ta ce ta ba da umarni ga wasu kamfanonin hada magunguna a kasar su fara samar da maganin zazzabin cizon sauro chloroquine domin yin gwajin ko zai magance cutar coronavirus.

    A wasu jerin sakwanni da ta wallafa a shafinta na twitter, NAFDA ta ce bayanai daga China na nuna cewa an ga tasirin maganin na chloroquine kuma an amince a yi amfani da shi wajen jinyar masu fama da coronavirus a kasar bayan jerin wasu gwaje-gwaje da aka gudanar a kasar ta China.

    Hukumar ta ce tuni ta umarci wani kamfani da ya fara samar da maganin na chloroquine a Najeriya ya kuma adana shi ko da za a bukace shi bayan kammala gwajin da ake yi a kasar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  15. Coronavirus: Sojoji na hana mutane fita a Abuja

    Sojoji

    A wasu sassan birnin Abuja, sojoji na tare mutane inda suke umartar su da su koma inda suka fito a ci gaba da umarnin gwamnati na zama a gida har makonni biyu.

    Da misalin karfe 11 na daren ranar Litinin ne dai dokar kunle ta fara aiki a birnin Abuja, inda aka samu masu dauke da cutar coronavirus 25.

    Sojoji
    Sojoji
    Sojoji
  16. An hana fita har tsawon wata daya a Akwa Ibom

    Gwamnatin jihar Akwai Ibom a kudancin Najeriya ta sanya hannu kan dokar da za ta hana wa mutanen jihar fita har na tsawon wata daya da kuma killace wadanda suka kamu da cutar coronavirus.

    Kamfanin dillacin labaran Najeriya NAN ya ce kwamishinan watsa labaran jihar Charles Udoh ne ya sanar da daukar matakin a wani taron manema labarai a ranar Talata.

    Ya ce tun a ranar Litinin da gwamnan ya sanya wa dokar hannu, ta fara aiki, kuma ya bukaci kwamishinan ‘yan sandan jihar ya dauki matakan tabbatar da dokar.

    Dokar za ta ci gaba da aiki har 30 ga watan Afrilu.

    Gwamnatin jihar ta akwa Ibom ta dauki matakan ne domin dakile yaduwar coronavirus duk da cewa zuwa yanzu babu wanda ya kamu da cutar a jihar.

    Gwamnan Akwa Ibom Udom Emmanuel

    Asalin hoton, NTA

  17. Ta yaya zan kare kaina daga kamuwa da coronavirus?

    Masana kiwon lafiya sun ce abin da ya fi kamata a yai shi ne yawan wanke hannu da ruwa da sabulu.

    Coronavirus tana yaduwa ne idan mutum da ke dauke da ita ya yi tari har kwayoyin cutar suka yadu a cikin iska.

    Da zarar wani ya shaki isakar ko kuma ya taba wajen da kwayoyin cutar suka fada akai, sannan ya taba idonsa ko hancinsa ko bakinsa, to zai iya kamuwa.

    Don haka yin tari da atishawa a cikin toli fefa, da gudun taba fuskarku da hannayen da ba a wanke ba, da kuma gujewa yin alaka ta kut da kut da mutanen da suka kamu na da matukar muhimmanci wajen hana yaduwar cutar.

    Kwararru a fannin lafiya sun ce takunkumin rufe fuska ba ya tasiri sosai wajen kariya.

    Bayanai kan coronavirus
  18. Coronavirus na iya durkusar da tsarin kiwon lafiyar Afrika - ICRC

    Kungiyar agaji ta Red Cross ta yi gargadin cewa tsarin kiwon lafiyar Afirka a sassan Afirka zai iya durkushewa saboda girman annobar cutar coronavirus.

    ICRC ta ce cibiyoyin lafiya da dama sun lalace a yankunan da ke fama da rikici.

    Ta ce a Mali kashi cas’in da uku na cibiyoyin lafiya sun lalace. A wasu wuraren kuma, ana fama da karancin ruwa mai tsafta da sabulun da ya kamata a wanke hannu domin dakile bazuwar coronavirus.

    Sannan tazara ko nisanta da juna da ake bukatar mutane su dinga yi yana da wahala ya yi tasiri a sansanonin ‘yan gudun hijira.

    Zuwa yanzu Afirka ita ce nahiyar da cutar ba ta yi wa illa ba sosai, amma yawan wadanda ke kamuwa da cutar da kuma wadanda ke mutuwa sai karuwa suke.

    An mayar da wasu filayen wasanni a matsayin cibiyoyin kula da masu coronavirus a Legas kudancin Najeriya

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, An mayar da wasu filayen wasanni a matsayin cibiyoyin kula da masu coronavirus a Legas kudancin Najeriya
  19. Coronavirus ta fara kamari a Syria

    Shugaban Hukumar ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadin cewa mutum 10 da aka tabbatar da sun kamu da coronavirus a Syria inda kuma mutum daya ya mutu, somin tabi ne.

    Mark Lowcock ya shaida wa kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya cewa cutar na iya tasiri sosai a tsakanin al’umma.

    Hukumomin Lafiya a Syria sun kasance masu rauni bayan shafe shekara tara cikin yaki, inda kusan rabin asibitoci da cibiyoyin shan magani ne kawai ke aiki.

    Manzo na musammanna Majalisar Dinkin Duniya Geir Pedersen ya yi kiran tsagaita buda wuta domin bayar da damar tunkarar yaki da coronavirus a sassan kasar.

    Mutum miliyan shida yakin Syria ya raba da gidajensu, kuma yawancinsu yanzu na rayuwa ne a sansanonin da suka cika makil.

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Mutum miliyan shida yakin Syria ya raba da gidajensu, kuma yawancinsu yanzu na rayuwa ne a sansanonin da suka cika makil.
  20. Covid-19: An sanya dokar ta-baci a Mozambique

    Shugaban Mozambique Filipe Nyusi ya sanar da sanya dokar ta-baci ta kwana 30, daga ranar Laraba, a kokarinsa na dakile yaduwar coronavirus a kasar.

    Za a tsaurara matakai kamar takaita zirga-zirgar jama'a da rufe kan iyaka da haramta tarukan jama'a, ciki har da taruka a wuraren ibada, a cewarsa.

    Za a killace mutanen da suka koma kasar daga kasashen waje, ko kuma wadanda suka yi mu'amala da su, in ji shugaban kasar a jawabin da ya gabatar a gidan talbijin din kasar ranar Litinin.

    Mozambique na da mutum takwas da suka harbu da Covid-19, biyu daga cikinsu a cikin kasar suka samu.

    Filipe Nyusi

    Asalin hoton, AFP