'An gano yawan mutanen da suka bata a Kano'
Kwamitin binciken gano yaran da suka bata da gwamnatin jihar Kano a Najeriya ta kafa ya ce ya gano adadin yawan mutanen da suka bata a jihar.
Shugaban Kwamitin mai shari'a Wada Rano yashaida wa BBC cewa kwamitinsa ya gano mutum 113 da suka tabbatar da sun bata a jihar daga 2010 zuwa 2019.
Ya ce ta hanyar iyayen da yaransu suka bata ne suka gano yawan adadinsu, kuma akwani wani gidan marayu da ake tafiyar da shi ba bisa ka'ida ba da aka gano wasu yaran da suka bata.
Ya kara da cewa daga cikin Yaran da aka gano har da wasu guda uku 'yan kabilar Igbo daga jihar Anambra a kudancin kasar.