Wani dan sandan Kenya wanda ake sa ran zai bayar da shaida game da badakalar sayo makaman soji da ta kai ta $395m, wadda aka yi ta tsakaci a kanta, ya mutu. An ga gawarsa ne a gidansa da ke, Nairobi, babban birnin kasar.
An ga harbin bindiga a goshin Sajan John Kipyegon Kemei, wanda ya yi aiki a ofishin mataimakin shugaban kasar, William Ruto.
Kafafen watsa labaran kasar sun ruwaito cewa dan sandan yana aiki ranar da tsohon ministan kasar ta Kenyan ya ziyarci ofishin mataimakin shugaban kasar tare da rakiyar wasu daraktoci daga wani kamfanin Amurka domin tattaunawa kan cinikin makamai.
Tuni dai aka tuhumi tsohon minsitan, Rashid Echesa, da laifin yin jabun takardun kwangila.
Kamfanin na Amurka Eco Advanced Technologies ya yi zargin cewa Mr Echesa ya mika musu yarjejeniyar kwangila ta jabu domin samar wa sojin Kenya makamai, yana mai zarginsa da damfarar su kusan $113,727 (£88,204).
An bayar da belin Mr Echesa bayan ya musanta zargin.